Thursday, August 6
Shadow
Kalli Bidiyon: Mahaifiyar Maimuna, Wadda Adam A. Zango ya saki ta yi bayani dalla-dalla kan abinda ya faru

Kalli Bidiyon: Mahaifiyar Maimuna, Wadda Adam A. Zango ya saki ta yi bayani dalla-dalla kan abinda ya faru

Duk Labarai
Mahaifiyar Maimuna watau matar da Adam A. Zango ya saki kwanannan ta yi magana kan yand sakin diyarta ya faru. Tace diyarta bata da laifi, hakanan Adam A. Zango bashi da laifi kan abinda ya faru. Tace maganar gwajin kwayoyin Halitta na Genotype da Adam A. Zango ya fada, ita ta hana ayi kamin aure dan tace su a lokacin da aka musu aure ba'a yi irin wannan bincikenba. https://www.tiktok.com/@78alhmohammed/video/7669584674712276232?_r=1&_t=ZS-98ZRoLT7fA0
Farashin dala a kasuwar Chanji ta yau, Litinin

Farashin dala a kasuwar Chanji ta yau, Litinin

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Litinin 3 ga watan Augusta na shekarar 2026 ya kamane akan Naira ₦1,368 akan kowace dala. A jiya, 2 ga watan Augusta kasuwar Gwamnatin an kulleta ne a farashi dalar yana akan Naira ₦1,368.22 akan kowace dala. A kasuwar bayan fage kuwa, Farashin dalar ya kamane akan Naira ₦1,410 akan kowace dala inda idan mutum saye zai yi kuma za'a sayar masa ne akan Naira ₦1,425 akan kowace dala.
Kalli Bidiyon: Idan ana ruwan sama Ladani yaje kiran sallah, idan yazo daidai Hayya Alassalah, zai cene Sallu fi biyutikum, watau ku yi sallah a gidajenku>>Inji Dr. Zakaria Buhari

Kalli Bidiyon: Idan ana ruwan sama Ladani yaje kiran sallah, idan yazo daidai Hayya Alassalah, zai cene Sallu fi biyutikum, watau ku yi sallah a gidajenku>>Inji Dr. Zakaria Buhari

Duk Labarai
Dr. Zakaria Buhari ya bayyana cewa, idan ladani ya je kiran Sallah ana ruwan sama, idan yazo daidai Hayya Alassalah. Sai yace Sallu fi biyutikum, watau ku yi sallah a gidajenku. Yace kokuma ladam zai iya cewa kowa yayi Sallah a inda yake dan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ne yace a yi hakan. https://www.tiktok.com/@dr_zakaria_bouhari/video/7668795302412930312?_r=1&_t=ZS-98ZInvqANyT
Aslam Aliyu ta kusa da Atiku Abubakar data bar ADC ta koma APC ta gana da shugaba Tinubu

Aslam Aliyu ta kusa da Atiku Abubakar data bar ADC ta koma APC ta gana da shugaba Tinubu

Duk Labarai
Aslam Aliyu wadda sananniyar ta kusa da Atiku Abubakar ce amma ta sanar da ficewa daga ADC ta koma APC a yanzu ta gana da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Aslam Aliyu wadda 'yar Jihar Zamfara ce ta mika hannu suka gaisa da shugaba Tinubu a yayin ziyarar data kai masa. https://twitter.com/i/status/2084061651649614109 Bayan fitarta daga ADC, Aslam da yaran Atiku sun yi ta musayar kalamai a tsakaninsu wanda har tace zatawa Atikun Tonon Silili. Saidai bata yi ba.
Kalli Bidiyon: Idan kayi mu’amala ta minti 5 da farfesa  Isa Ali Pantami sai ka ji ba dadi, bashi da mu’amala me kyau amma yana da ilimin addini>>Inji Affan Buba Abuya

Kalli Bidiyon: Idan kayi mu’amala ta minti 5 da farfesa Isa Ali Pantami sai ka ji ba dadi, bashi da mu’amala me kyau amma yana da ilimin addini>>Inji Affan Buba Abuya

Duk Labarai
Affan Buba Abuya ya bayyana cewa, yayi aiki tare da Farfesa Sheikh Isa Ali Pantami har sau biyu, a yayin da yana shugaban ma'aikatar NITDA da kuma Minista. Yace Malam na da ilimin addini amma bashi da mu'amala me kyau. Yace dalili ma da yasa kenan yace ba zai goyi bayansa da ya fito takarar Gwamnan jihar Gombe ba. Yace Pantami mutane kan so su ganshi lokacin yana Minista amma sai yaki, yace har rana aka ware ta ganawa da mutane amma daga baya yace a daina, yace duk sanda yake son ganawa da wani zai gaya masa. Yace idan zasu je Gombe yakan cewa Malam a tanadi kudi da za'awa mutane hidima amma sai malam yace bai yadda ba. Yace daga aljihunsa yakan cirewa ya bayar da sunan malam. https://twitter.com/i/status/2084050521963339991
Tinubu baya son gaskiya, an gaya masa yaki ji, kuma hakan zai sa ya fadi zaben 2027>>Inji Primate Ayodele

Tinubu baya son gaskiya, an gaya masa yaki ji, kuma hakan zai sa ya fadi zaben 2027>>Inji Primate Ayodele

Duk Labarai
Babban Malamin Coci Primate Ayodele ya bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu baya son a gaya masa gaskiya. Ya jinjinawa limaman cocin Katolika da suka je har fadar ahugaban kasar suka gaya masa halin da 'yan Najeriya ke ciki. Yace gaskiyace 'yan Najeriya na cikin wahala ko yaji ko karya ji wannan ya rage nasa amma an gaya masa gaskiya. Yace kuma shugaban kasar zai fadi zabe a 2027, na kusa dashi zasu kaishi su baro Yace kuma abin ba zai masa dadi ba. https://twitter.com/i/status/2084029111782269342
Kalli Bidiyon: Yanda Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila da Gwamnan Lagos Sanwo Olu ke buga Kwallo

Kalli Bidiyon: Yanda Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila da Gwamnan Lagos Sanwo Olu ke buga Kwallo

Duk Labarai
An hangi Gwamnan Lagos, Sanwo Olu da shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila suna buga kwallo. Sun rika fasin fasin inda daga karshe Gbajabiamila ya saka kwallon a raga. https://twitter.com/i/status/2083935818771521904 Saidai masu suka sun ce hakan bai dace ba lura da cewa wannan abu da suke babu ta yanda zai amfani Talaka.