An samu babbar Baraka a jam’iyyar APC inda wasu suka fito suka ce basu tare da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu
Tsohon Ministan Shari'a na Najeriya, Dakta Abubakar Malami, SAN, ya yi watsi da iƙirarin da wasu ƴan tsohuwar jam'iyyar CPC - da ta narke cikin haɗakar APC - suka yi na nesanta tsohuwar jam'iyyar daga ficewa daga haɗakar.
A farkon makon nan ne wani tsagin tsohuwar jam'iyyar CPC ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamnan Nasarawa, Umaru Tanko Almakura suka yi taro a Abuja, inda suka jaddada goyon bayansu ga gwamnatin shugaba Tinubu tare da nesanta kansu daga ficewa daga APC.
Daga cikin waɗanda suka harci taron har da tsohon gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari da tsohon ministan Ilimi, Mallam Adamu Adamu da Hon Farouk Adamu Aliyu, tsohon ɗan majalisar daga jihar Jigawa da wasu ƙusushin tsohuwar CPCn.
To sai toshon Ministan ya yi watsi da wannan iƙirari da tsagin Almakuran suka yi, yana mai...








