Wannan Alh. Ibrahim Mijinyawa ne mamallakin manyan shagunan Sahad stores dake Kaduna, Kano,Abuja, Da Nasarawa.
Rahotanni sun ce bashi da girman kai sam kuma baya cin bashin banki sannan yana kyautatawa ma'aikatansa sosai.
Kuma yana kokarin fitar da Zakka.
Mutane 10 sun mutu da dama sun jikkata a wani mummunan hadarin mota da ya faru a jihar Jigawa.
Lamarin ya farune a karamar hukumar Taura dake jihar.
Wani Shaidar gani da ido ya gayawa manema labarai cewa hadarin ya farune a kauyen 'Yanfari dake kan hanyar Kano zuwa Hadejia a karamar hukumar Taura.
Yace motar bas ce ta daki wata Tirela dake a gefen titi inda motar ta wuntsula mutane 10 suka mutu nan take.
Kakakin 'yansandan jihar, DSP Lawan Shiisu ya tabbatar da faruwar lamarin.
Yace lamarin ya farune ranar November 12, 2024 kuma suna samun labari jami'an su suka garzaya wajan inda yace sun tarar direban motar da mutane 9 sun mutu.
Yace akwai mutum da ya da bai mutu ba a yanzu ana duba lafiyarsa.
Yace suna kan bincike dan gano ko akwai laifin wani a hadarin da ya faru.
Shugaban rukunin Kamfanin Mai Na NNPC, Mele Kyari ne ya bayyana nasarar kammala biyan bashin da ake bin kamfanin da ga kamfanonin mai na kasashen ƙetare inda ya ce a yanzu, babu mai bin kamfanin bashin sisin kwabo.Kyari ya ce, wannan babban nasara ce da aka cimma biyo bayan cire tallafin mai a Gwamnatin Shugaba Tinubu.
“Mun rika karkatar da kudadenmu da dukiyoyinmu don tabbatar da komai na tafiya daidai a bangaren mai na PMS mai wuyar sha'ani, abinda ya rika janye hankalin NNPC daga biyan basussuka"
Mele ya ci gaba da cewa“ Sai dai yanzu wannan matsala ta kau, za ku ga cewa ba mu da wani bashin da ake bin mu, kuma don mu tabbatar da dorewar hakan, ya zama wajibi a kawar da duk wata matsala don masana'antar ta iya samar da makamashi mai dorewa da arha da ake buƙata a ƙasar nan."
Sh...
Hukumar 'yansanda a Birnin Jos na jihar Filato ta tabbatar da fargabar dasa bam a birnin.
Saidai ta musanta wannan jita-jita.
Kakakin 'yansandan jihar, DSP Alfred Alabo ya tabbatarwa manema labarai cewa maganar dasa bam din ba gaskiya bane.
Yace ranar Talata ne aka fara yada jitajitar kuma jami'an su da suka kware wajan kula da bam sun isa wajan inda suka tabbatar da babu bam a inda ake rade-radin.
Infection na mata da suke fama dashi a gabansu abu ne wanda ya zama ruwan dare, a wani binciken masa na jami'ar Harvard sun bayyana cewa kaso 75 cikin 100 na mata sun taba samun ko kuma zasu samu cutar Infection a rayuwarsu.
Tafarnuwa na taimakawa sosai wajan magance matsalar cutar Infection tana hana abinda ke zama a farjin mace ya bata infection yaduwa.
Infection din gaban mata ana kiransa da Yeast infection a turance, shi Yeast din wani ruwa ne da a gaban kowace mace akwaishi, amma akan samu matsala wani lokacin sai yayi yawa sosai shine sai ya koma ya zama infection.
Ga alamomin da mace zata gane tana da cutar Infection kamar haka:
Idan kika ji gabanki na kaikai ko yana miki ba dadi.
Idan kina jin zafi yayin jima'i.
Idan farin ruwa me kauri na fita daga gabanki.
A...
Wani magidanci ya gano abokinsa na lalata da matarsa wadda suka shafe shekaru 8 da aure.
Mutumin ya gano hakane bayan da yayi gwajin kwayoyin halitta wanda ake cewa DNA.
https://www.youtube.com/watch?v=AmOmF-r4F7E
Bidiyon mutumin ya watsu sosai a kafafen sda zumunta inda aka ta tayashi Alhini.
Tauraruwar Fina-finan Hausa, Mansurah Isa kenan a wadannan hotunan nata data sha kyau.
Ta sakawa masoyanta hotunan a shafinta na sada zumunta inda suka yaba.
Rahotanni sun nuna cewa jimullar bashin da ake bin Najeriya ya nuna cewa kowane dan kasa ana binshi bashin Naira N619,501.
Bayanai daga ofishin dake kula da bashin Najeriya sun nuna cewa ana bin Najeriya jimullar bashin Naira Tiriliyan N134.297.
Bashi dai na daya daga cikin hanyoyin da gwamnati ke bi dan samun kudin shiga wanda ake gudanar da ayyukan raya kasa dasu.
Kamfanin Man fetur na kasa,NNPCL ya dakatar da sayo man fetur daga kasar waje inda ya amince ya sayi man fetur din daga wajan Matatar man fetur din Dangote da sauran matatun man fetur masu zaman kansu.
Shugaban kamfanin, Mele Kyari ya bayyana haka a wajan wani taro da ya faru a Legas ranar Litinin.
Hakan na zuwane yayin da 'yan kasuwar man fetur suka nace saidai su sayo man fetur din daga kasar waje maimakon sayowa daga hannun matatar man Dangote saboda a cewarsu,man fetur din da suke kawowa daga wajen ya fi na Dangote sauki.
Kyari ya kuma musanta cewa suna yiwa matatar man fetur ta Dangote zagon kasa inda yace suma suna da hannun jari a matatar.
Hukumar yaki da rashawa da cin hanci ta kasa, EFCC ta gayyaci wani dan kasar Nijar me suna Ibrahim Mohammad saboda yanda aka yi liken kudi a wajan bikinsa.
Hakan ya biyo bayan watsuwar Bidiyon bikin a kafafen sada zumunta inda aka rika kiran EFCC da ta dauki mataki akan lamarin.
Kakakin hukumar, Dele Oyewale ya fitar da sanarwa akan lamarin inda yace da farko an danganta bikin da diyar Danjuma Goje me suna Fauziyya amma daga baya da aka yi bincike an gano bikin na Hajara Seidu Haruna ne wadda ke harkar GwalaGwalai a Kano, Abuja da Dubai.
Yace wadanda ake zargin sun amsa laifinsu.