Sunday, July 12
Shadow
Hukumar ‘Yansandan Najeriya sun yi magana kan Zàngà-Zàngàr da ake shirin yi gobe ta Adawa da wasu tsare-tsaren gwamnatin Tinubu

Hukumar ‘Yansandan Najeriya sun yi magana kan Zàngà-Zàngàr da ake shirin yi gobe ta Adawa da wasu tsare-tsaren gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Hukumar 'yansanda a jihar Legas sun fitar da sanarwa game da zanga-zangar da ake shirin yi gobe a fadin Najeriya. Hukumar 'yansandan ta gargadi masu zanga-zangar kada wajan gudanar da zanga-zangar su rika hayewa 'yansanda suna cin zarafinsu. Kungiyar TIB da wasu kungiyoyin ne suka shirya wannan zanga-zangar inda suka ce suna so ne a soke dokar saka ido a kafafen sada zumunta da yanar gizo da kuma janye dakatarwar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yawa gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara. Saidai a sanarwar da hukumar 'yansandan jihar Legas din ta fitar ta bakin kakakinta wadda DCP Tijani O. Fatai ya sakawa hannu, yace sun lura da cewa, ana amfani da wahalar da ake ciki wajan jawo mutane su fito zanga-zangar. Ya bayyana cewa, zasu saka mutanensu a gurare daban-daban na fadin j...
Tsohuwar Ministar Jin Kai, Betta Edu da aka sauke saboda zargin karkatar da kudin Talakawa ta samu kyautar girmamawa a jami’ar Calabar

Tsohuwar Ministar Jin Kai, Betta Edu da aka sauke saboda zargin karkatar da kudin Talakawa ta samu kyautar girmamawa a jami’ar Calabar

Duk Labarai
Tsohuwar minister Jin kai, Betta Edu wadda aka sauke saboda zargin karkatar da kudaden talakawa ta bayyana a wajan bikin cika shekaru 50 da kafuwar jami'ar Calabar dake jihar Cross-River. Wani abin mamaki shine har kyautar karramawa aka baiwa ministar. Da yawa sun yi mamakin ganin Ministar a bainar jama'a tana ta sha'aninta. Kyautar da aka bata itace ta tallafawa al'umma da ta yi. Daga cikin zarge-zargen kudaden da akawa ministar a baya sun hada da na Naira Miliyan N585 da kuma na Dala $640,000. A baya dai tsohuwar ministar ta kuma shiryawa Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero shan ruwa a gidanta.
Yansanda Sun Cafke Jami’insu Da Ya yi Barazanar Ramuwar Gayya Kan Kìsàn Mafarauta a Edo

Yansanda Sun Cafke Jami’insu Da Ya yi Barazanar Ramuwar Gayya Kan Kìsàn Mafarauta a Edo

Duk Labarai
‘ Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta cafke Hadaina Dan-taki, wanda ya yi barazanar kai hari ga ‘yan kudu a Arewa, domin daukar fansa kan mafarauta 16 da aka kashe a Uromi, jihar Edo. Hakan ya biyo bayan cece-kucen da jama’a suka yi akan jami'an bayan wallafa sakon barazanar a shafinsa na Facebook. Idan zamu iya tunawa dai dan sandan ya yi barazanar kai harin ramuwar gayya ga 'yan kudancin Najeriya da ke zaune a arewacin Najeriya. Kalaman Dan-Taki na zuwa ne a matsayin martani ga kashe ‘yan Arewa 16 da aka yi a garin Uromi dake Jihar Edo. A wani zazzafan tsokaci da ya yi a Facebook ranar Talata, Dan-Taki ya rantse da Allah sai ya rama kisan da aka yiwa al'ummar Arewa, yana mai shan alwashin cewa ‘yan Arewa za su dauki kwakkwaran mataki kan ‘yan Kudu a nan gaba kaɗan. ...
Al’ummar Kano Sun Zargi ‘Yansanda Da Yunƙurin Sanya Dokar Ta-baci Kan Gayyatar Sarki Sunusi

Al’ummar Kano Sun Zargi ‘Yansanda Da Yunƙurin Sanya Dokar Ta-baci Kan Gayyatar Sarki Sunusi

Duk Labarai
Al'umma Jihar Kano sun yi ikirarin cewa gayyatar da babban Sifetan 'yansanda ya yi wa Sarki Sanusi wani bangare na shirin kafa dokar ta-baci a Jihar. Hakan na zuwa ne biyo bayan rahotannin da ke cewa rundunar ‘yan sandan Najeriya ta gayyaci Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, a hukumance, zuwa ofishin ta dake Abuja domin bincike kan wani yamutsu da aka samu a lokacin bukukuwan Sallah. Wasu ‘yan jihar da suka yi magana kan kama Usman Sagiru dan shekara 20 a ranar Lahadi, 30 ga Maris, 2025 da ke Sharifai Quarters dangane da zargin kisan wani dan banga a tawagar Sarki Sanusi Lamido Sanusi na biyu bayan Sallar Idi, sun bayyana cewa ba za su iya alakanta lamarin da gayyatar Sarki ba. Takardar gayyata mai kwanan wata 4 ga Afrilu, 2025, kuma mai dauke da sa hannun CP Olajide Rufus Ib...
Kalli Yanda Zanga-zangar “Takalmin Annabi ya fi kowa” ta barke a Katsina

Kalli Yanda Zanga-zangar “Takalmin Annabi ya fi kowa” ta barke a Katsina

Duk Labarai
Daga Auwal Isa Musa Kamar yadda wakilin Jaridar Taskar Labarai taskar labarai ya aiko mana, cincirindon jama'a ne suka yi farin-dango wajen fitowa tare da bazama a kan manyan Titunan birnin Katsina da hantsin yau Asabar, domin gudanar da zanga-zanga maintaken "Takalmin Annabi ya fi kowa" Bangarorin al'ummar musulmi a jihar ta katsina, an shaida shigarsu wannan zanga-zanga wadda yanzu haka take gudana a tsanake, a yain da mahalartanta ke rera wakokin yabo ga fiyayyen halitta, musamman Takalminsa (S) da suka fito zanga-zangar nuna daraja da fifikonsa. Zanga-zangar ta taso ne taso ne daga filin Polo/kofar 'yandaka, inda ta ta nufo cikin gari.
Na Yafe Duk Wata Rashin Fahimta Da Ta Shiga Tsakanina Da Marigayi Sheik Idris Dutsen Tanshi, Inji Gwamna Bala Mohammed yayin da yaje ta’aziyyar malamin

Na Yafe Duk Wata Rashin Fahimta Da Ta Shiga Tsakanina Da Marigayi Sheik Idris Dutsen Tanshi, Inji Gwamna Bala Mohammed yayin da yaje ta’aziyyar malamin

Duk Labarai
Na Yafe Duk Wata Rashin Fahimta Da Ta Shiga Tsakanina Da Marigayi Sheik Idris Dutsen Tanshi, Inji Gwamna Bala Mohammed …Malami ne mara tsoro da ya sadaukar da rayuwarsa wajen karantar da mušùĺùnçìn, wanda jihar Bauchi za ta yi kewarsa …ya ku mallakawa Almajiransa filin game village Daga Rariya A yammacin yau Abasar ne Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed ya kai ziyarar ta'aziyyar rasuwar Sheik Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi ga iyalansa da mabiyansa, wanda ya rasu a daren Juma'ar da ta gabata. Gwamna Bala wanda ya jagoranci tawagar mukarraban gwamnati, ya kai ziyarar ta'aziyyar ne a madadin kansa, iyalansa, gwamnati da kuma daukacin al'ummar jihar Bauchi. Gwamnan ya bayyana marigayi Shehin Malamin a matsayin malamin mara tsoro wanda ya sadaukar da kansa waj...
Bashin da ake bin Najeriya ya karu sosai

Bashin da ake bin Najeriya ya karu sosai

Duk Labarai
Bashin da ake bin Nijeriya ya haura zuwa tiriliyan N144.67 a 2024 - Rahoton DMO Ofishin kula da basussuka na Nijeriya ya ce bashin da ake bin Najeriya ya karu da naira tiriliyan N47.32tn, wanda ya nuna karuwar kashi 48.58 cikin 100 daga Disamba 2023 zuwa Disamba 2024. Sabon rahoton da aka fitar a wannan Juma’a, ya nuna cewa an samu karuwar cin bashi daga kasashen waje da kuma cikin gida, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
An min Wahayi cewa nan gaba a saman wata da kuke gani a sama zamu je mu yi zaman taro>>Inji Pastor Enoch Adeboye

An min Wahayi cewa nan gaba a saman wata da kuke gani a sama zamu je mu yi zaman taro>>Inji Pastor Enoch Adeboye

Duk Labarai
Babban Malamin kirista, Pastor Enoch Adeboye ya bayyana cewa, an masa wahayi cewa, nan gaba a saman wata za'a je a gudanar da taron cocinsa. Faston ya bayyanawa mabiyansa hakane yayin da yake musu wa'azi. Saidai yace lamarin Allah akwai ban mamaki amma ba lalai bane sai mutane sun yarda ba. Lamarin dai ya baiwa mutane da yawa, ciki hadda kiristoci mamaki.
Kalli matashi me digiri na 3 watau Ph. D da ke aikin goge-goge ana biyanshi Albashin Naira Dubu 70

Kalli matashi me digiri na 3 watau Ph. D da ke aikin goge-goge ana biyanshi Albashin Naira Dubu 70

Duk Labarai
Wannan wani mutum ne a jami'ar jihar Ebonyi me suna Dr. Enyi onyebuchi Paul wanda a shekarar 2007 ya samu aikin goge-goge a makarantar. Saidai ya jajirce inda ya ci gaba da karatu har ya samu Digiri na daya zuwa na 3 a makarantar. Saidai duk da wannan kokari da yayi, ba'a mayar dashi malami me koyarwa ba a jami'ar. An ci gaba da barinsa a matsayin me goge-goge inda ake biyansa Albashin Naira Dubu 70. An dai yi zargin saboda bashi da kafa ne shiyasa ya kasa samun aikin koyarwa a makarantar.
Matashi Ba Taliya Ko Ƴan Kuɗi Yake Buƙata Daga Wajen Ƴan Siyasa Ba Face A Gina Rayuwarsa-Inji Sanata Ahmad Babba Kaita

Matashi Ba Taliya Ko Ƴan Kuɗi Yake Buƙata Daga Wajen Ƴan Siyasa Ba Face A Gina Rayuwarsa-Inji Sanata Ahmad Babba Kaita

Duk Labarai
Daga Comr Nura Siniya Tsohon Sanata mai wakiltar shiyyar Daura a jihar Katsina Sen. Ahmad Babba Kaita, ya bayyana cewa matashin Najeriya ba Taliya ko 'yan kudi yake bukata daga wajen 'yan siyasa face a gina rayuwarsa don gobensa ta yi kyau. A cewar sa, Sanata Kaita rayuwar matasa a Najeriya ba za ta inganta da taliya ko kyautar naira daga hannun ‘yan siyasa ba. Ya kuma ce abubuwan da matasa ke buƙata da gaske sune: tsaro mai kyau, ingantaccen ilimi da kuma samun aikin yi ko sana'ar dogaro da kai. Sanatan ya jaddada cewa waɗannan ginshiƙai su ne tushen da ya gina siyasarsa a kai, kuma yana fatan ci gaba da bin wannan hanya don ganin rayuwar matasa A ƙarshe ya ce Ina siyasa ne don a gina rayuwar matasa. Ba wai domin jama’a su sa ni a dama da su ba. Ina fatan ganin matasan Najeriy...