Sunday, April 26
Shadow
Sojoji sun ce sun lalata sansanin Bello Tùrjì tare da kkashe ‘yànbìndìgà 25

Sojoji sun ce sun lalata sansanin Bello Tùrjì tare da kkashe ‘yànbìndìgà 25

Duk Labarai
Rundunar sojin Najeriya ta ce ta samu nasarar lalata sansanin gawurtaccen ɗan bindigar nan Bello Turji a yankin Fakai na ƙaramar hukumar Shinkafi. Cikin wata sanarwa da jami'in hulda da jama'a na rundunar da ke yaƙi da 'yanbindiga a arewa maso yamma 'Operation Fansan Yamma' ya fitar, ya ce dakarun sojin sun ƙaddamar da hare-haren ne kan maɓoyar 'yanbindigar a ranar 10 ga watan Janairu. ''Bisa taimakon dakarun sojin sama, mun samu nasarar lalata sansanonin wasu 'yanbindiga a yankin Fakai na ƙaramar hukumar Shinkafi'', in ji sanarwar. Ya ƙara da cewa daga cikin sansanonin da aka lalata har da na Bello Turji da Mallam Ila, inda aka kashe 'yanbindiga 25 tare da raunata fiye da 18. Haka ma ya ce a lokacin samamen sojojin sun kuɓutar da mutum bakwai da 'yanbindigar suka yi garkuwa da...
Ɓangaren Aminu Ado Bayero ya ce zai ɗaukaka ƙara

Ɓangaren Aminu Ado Bayero ya ce zai ɗaukaka ƙara

Duk Labarai
Bangaren sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce zai ɗaukaka ƙara kan hukuncin da kotun ɗaukaka ta yanke kan dambarwar masarutun jihar. A ranar Juma’a ne kotun ɗaukaka ƙara ta yankee hukuncin cewa babbar kotun tarayya – da ta yi hukuncin dakatar da gwamnatin Kano daga soke masarautun jihar – ba ta da hurumin sauraron ƙarar da ta shafi masarautu a jihar. To sai dai a wani taron manema labarai da Aminu Babba Dangundi – wanda tun da farko ya shigar da gwamnatin Kano ƙara a madadin masarautun da aka rushe – ya yi, ya ce za su ɗaukaka ƙara kan hukuncin. Ya ce tun da farko gwamnatin Kano da majalisar dokokin jihar ba su bi ƙa’ida ba wajen soke masarautun jihar. ‘’Bai kamata a sauke sarki ba tare da ba shi damar kare kansa daga laifin da aka zarge shi a kai ba’’, in ji shi. ...
A yayin da Gobarar California kasar Amurka ke ci gaba da yaduwa, an hango wata mahaukaciyar Guguwa ta taho zata rura wutar ta kara shiga cikin gari dan ci gaba da kona gidaje

A yayin da Gobarar California kasar Amurka ke ci gaba da yaduwa, an hango wata mahaukaciyar Guguwa ta taho zata rura wutar ta kara shiga cikin gari dan ci gaba da kona gidaje

Duk Labarai
Wata mahaukaciyar guguwa da aka sakawa sunan Santa Ana winds dake gudun mita 45 duk awa ta doso garin Los Angeles dake ci da wuta. Ana tsammanin wannan guguwa zata rura wutar inda zata turata zuwa sassan garin dake da muhimmanci kamar gidan tarihin garin me suna J. Paul Getty Museum da kuma jami'ar University of California. Tuni dai aka fitar da sanarwa ga mutanen dake yankin da su fice daga gidajensu. Zuwa yanzu dai gobarar ta kone sama da gidaje dubu goma sha biyu da kuma yin sanadin kisan mutane 16 inda mutane 13 sun bace ba'a san inda suke ba.
Gobarar Amerika: Yawan wadanda suka mutu sun karu a yayin da mahaukaciya Gobarar ke ci gaba da yaduwa

Gobarar Amerika: Yawan wadanda suka mutu sun karu a yayin da mahaukaciya Gobarar ke ci gaba da yaduwa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa yawan wanda suka mutu a ci gaba da yaduwar mahaukaciyar gobarar garin Los Angeles na kasar Amurka na ci gaba da karuwa. Zuwa yanzu mutane 16 ne hukumomi suka tabbatar da cewa, sun mutu a gobarar. Kamfanin dillancin labaran AP yace biyar daga cikin wadanda suka mutu a unguwar Palisades ne sai 11 kuma a unguwar Eaton sannan kuma mutane 13 sun bace ba'a san inda suke ba. Zuwa yanzu gidaje dubu talatin da biyar ne suke cikin duhu babu wutar lantarki sanadiyyar gobarar. Sama da masu aikin kashe gobara dubu goma sha hudu ne ke ta aiki ba dare ba rana dan hana gobarar yaduwa. Hutudole ya kawo muku cewa, yawan wanda ke kashe gobarar sun yi kadan ta yanda saida aka fito da masu laifi daga gidan yari dan su taimaka
Gobarar California: Masu kashe gobara sun yi kadan, an fito da masu laifi daga gidan yari dan su taimaka

Gobarar California: Masu kashe gobara sun yi kadan, an fito da masu laifi daga gidan yari dan su taimaka

Duk Labarai
Masu kashe mahaukaciyar gobarar garin Los Angeles na jihar California a kasar Amurka sun yi kadan duk da yawansu ya kai dubu bakwai da dari biyar. Lamarin yayi kamari ta yanda saida aka fito da masu laifi da ake tsare dasu a gidan yari dan su taimaka. A rahoton NPR, tace masu laifi sama da 900 ne aka fito dasu daga gidan yari dan su taimaka a kashe gobarar da taki ci ta ki cinyewa. Hakanan rahotanni sun tabbatar da cewa, kasar Mexico dake makotaka da kasar ta Amurka ma ta aika da ma'aikatan kashe Gobara dan su taimaka a kashe mahaukaciyar gobarar. A baya dai, hutudole ya kawo muku cewa ana tsaka da fama da wannan gobara kuma sai ga girgizar kasa a jihar ta California. Sama da mutane 5000 ne suka shaida cewa sun ji motsin kasa San Francisco bay dake da nisan mil 350 da garin...
Gobarar Amurka: Yayin da suke tsaka da fama da mahaukaciyar gobara an kuma samun girgizar kasar a California ta kasar Amurka

Gobarar Amurka: Yayin da suke tsaka da fama da mahaukaciyar gobara an kuma samun girgizar kasar a California ta kasar Amurka

Duk Labarai
Girgizar kasa me maki 3.7 ta auku a jihar California ta kasar Amurka yayin da jihar ke kan fama da matsalar mahaukaciyar gobara data kone gidaje sama da dubu 10. Girgizar kasar ta farun da safiyar ranar Juma'a a San Francisco Bay kuma sama da mutane dubu biyar sun ce sun ji wannan girgizar kasa. Girgizar ta farune a garin dake da nisan mil 350 da garin Loas Angeles. A kalla mutane 16 ne hukumomi suka tabbatar sun mutu gobarar Los Angeles.
Talauci alamace ta yawan zunubi da rashin tsoron Allah>>Inji Pasto Komayya

Talauci alamace ta yawan zunubi da rashin tsoron Allah>>Inji Pasto Komayya

Duk Labarai
Pastor Korede Komaiya ya bayyana cewa, talauci alamace ta rashin tsoron Allah da yawan zunubi. Faston ya bayyana hakane ga mabiyansa a cikin cocinsa. Yace a rubuce yake cewa, wadanda suka bi Allah, zasu samu rayuwa ta jin dadi. Dan haka yace talauci alamace ta rashin tsoron Allah da yawan zunubi. Bidiyon da yake wannan magana ya yadu sosai a kafafen sda zumunta inda akai ta masa raddi. Yace yawanci ba'a sanin ainahin halin mutum sai idan ya samu kudi. Ya kara da cewa, yawanci talakawan da zaka ga suna kankan da kai, dama ce basu samu ba.
Obasanjo da Yakubu Gowon sun goyi bayan kungiyar su shekarau dake son kwace mulki daga hannun Tinubu  shekarar 2027

Obasanjo da Yakubu Gowon sun goyi bayan kungiyar su shekarau dake son kwace mulki daga hannun Tinubu shekarar 2027

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kungiyar su tsohon Gwamnan Kano kuma sanata Ibrahim Shekaru me suna LND dake son rikidewa zuwa ta siyasa, ta samu goyon bayan tsaffin shuwagabannin Najeriya, Yakubu Gowon da Olusegun Obasanjo. Kungiyar dai na ci gaba da tuntubar manyan 'yan siyasa dga yankunan Kudu maso yamma da kudu maso kudu da kudu maso gabas dan cimma burinta. Shugaban kungiyar, Dr Umar Ardo ya tabbatar da komawarta ta siyasa dan samar da Jam'iyya me karfi da hadin kai da zata karade kowane yanki a kasarnan. Duka shuwagabannin biyu, Yakubu Gowon da Olusegun Obasanjo sun yi na'am da wannan tafiya inda suka bayar da shawarar mayar da ita ta kasa baki daya.