Rahotanni da hutudole ke samu na cewa an gyara wutar lantarkin babban birnin tarayya Abuja.
Hukumar TCN ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta yi.
Tacw sauran yankunan ma ana kan kokarin gyara wutar tasu.
Gwamnatin tarayya tace nan da shekarar 2027 zata samar da wutar Lantarki ta awanni 20 kullun.
Saidai tace sharadin hakan shine sai ta samu maau zuba jari a bangaren Fetur da iskar gas wanda a yanzu babu su sosai.
Me baiwa shugaban kasa shawara akan makamashi, Olu Verheijen ce ta bayyana haka a wata ziyara da ta kai kasar Africa ta kudu.
Tace za'a mayar da hankali ne wajan samarwa Birane da masana'antu karfin wutar lantarkin.
Innalillahi Wainna ilaihi Raji'un
Yanzu Yanzu Gobara ta tashi a kasuwar kantin kwari (Thaiba General Enterprise LTD).
Ubangiji Allah Maɗaukakin Sarki ya mayar da mafificin alherin abin da aka rasa.
MAGANIN SANYI KOWANE IRI INSHA ALLAH
Ga masu fama da ciwon sanyi kowanne iri ne insha Allah in suka bi wannan hanya zasu samu sauki,ko masu yawan tari da nura da ciwon gobobi da rikewar baya da kwankwaso da kaikayin jiki dadai sauran illolin da sanyi ke haifar wa.
ABIN DA ZAA NEMA.
Garin Tafarnuwa
2.Nono mekyau madara ta ruwa mekyau)
YADDA ZAA HADA
Zaa samu garin Tafarnuwa mai kyau sai a debi chakali daya a zuba a nono rabin kofi a juya asha da safe haka ma zaai da yamma,wato sau biyu a rana.
Insha Allah indai an samu garin mai kyau akai kamar na sati 2 zaaga Nasara sosai cikin YARDAR ALLAH
Allah yabada lafiya da zaman lafiya
Wani mutum ya dauki hankula bayan da yayi amfani da Hakoransa masu karfi ya daga wata mata sama.
https://www.youtube.com/watch?v=onX2QD08Nu0
Dan Najeriyar dai ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta bayan faruwar lamarin.
Rahotanni sun bayyana cewa, wutar Lantarkin Najeriya ta sake lalacewa a Yau Alhamis, 7/11/2024.
Hutudole ya samu rahoton cewa wutar lantarkin ta lalace ne da misalin karfe 11:20am na yau Alhamis.
Hukumar Nigeria National Grid ce ta tabbatar da hakan
Wannan ne karo na biyu da wutar ta lalace a cikin satin da muke sannan karo na 12 a cikin wannan shekarar da muke ciki.
Wakilan Hukumar zaben Najeriya, INEC sun ke kasar Amurka dan saka ido akan zaben kasar daya wakana.
Al'adace ta INEC din taje kasashen da ake zabe dan saka ido hakanan kuma itama takan gayyato wakilan kasashen Duniya dan su zo su saka ido a zaben Najeriya.
Mataimakin kakakin majalisar Dattijai, Sanata Barau I. Jibrin ya sanar da komawar Tauraruwar Fina-finan Hausa, Asma'u Abdullahi Wakili zuwa jam'iyyar APC.
Ya wallafa hakane a shafinsa na zada zumunta inda ya yi mata maraba zuwa jam'iyyar APC.
https://twitter.com/barauijibrin/status/1854270065547329955?t=7dvUTEwRZF-CKrPmAxoNAQ&s=19
Asma Wakili dai Hadimace ga gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf saidai ta ajiye mukamin nata inda ta kuma fice daga jam'iyyar NNPP zuwa jam'iyyar APC.
Sanata Barau yace Asma Wakili ta sanar da ficewarta daga NNPP a yayin ziyarar data kai masa a Abuja.
Barau ya kara da cewa Asma Wakili ta bayyana ayyukan alkhairi na jam'iyyar APC ne ya jawo ta zuwa jam'iyyar.
Yayi kira a gareta data zama jakadiya ta gari ga Masana'antarta ta Kannywood, Jam'iyy...
Sanata Shehu Sani daga jihar Kaduna ya bayyana ra'ayinsa akan mutuminnan na kasar Equatorial Guinea da yayi lalata da mata da yawa ya kuma dauki Bidiyon faruwar lamarin.
Sanata Sani yace Dalilin da yasa ake samun irin mutumin masu lalata da matan mutane a Ofis shine mata basu son mata 'yan uwansu su zama ogannin su.
https://twitter.com/ShehuSani/status/1854454657164156931?t=Y3ueoL-V8O9o9aKXhIBBWw&s=19
Lamarin mutumin ya dauki hankula sosai inda akai ta Allah wadai dashi inda wasu suka rika yaba masa.
Manyan 'yan kasuwar man fetur su A.A Rano, AYM Shafa da Matrix Petroleum Services Limited sun kai Aliko Dangote kotu inda suke bukatar kotu kada ta amince masa da bukatar da yayi na a hanasu siyo man fetur daga kasashen waje saidai su siya a hannunshi.
Dangote dai ya shigar da 'yan kasuwar da NNPCL kotu inda yake neman kotun ta hana shigo da man fetur daga kasar waje a rika saya daga hannunsa.
Dangote yace kawai ya kamata a shigo da man fetur Najeriya ne idan babu shi a matatarsa ko idan an samu karancinsa.
Saidai su kuma 'yan kasuwar sun bayyana cewa Dagote na son ya zama shi kadai ne ke rike da harkar man a kasarnan wanda haka ba zai haifarwa kasuwar da mai ido ba.
Sun ce idan aka baiwa Dangote wuka da nama na harkar zai zama shi kadai ne ke kayyade farashin wanda hakan bai k...