Wednesday, February 18
Shadow
Allah Sarki: Ji Dalilin da yasa Yusuf Buhari bai ce uffan ba kan rayuwar mahaifinsa a littafin tarihin rayuwar mahaifinsa, Muhammadu Buhari da aka rubuta

Allah Sarki: Ji Dalilin da yasa Yusuf Buhari bai ce uffan ba kan rayuwar mahaifinsa a littafin tarihin rayuwar mahaifinsa, Muhammadu Buhari da aka rubuta

Duk Labarai
A yayin da ake ta jin abubuwan da suka faru a rayuwar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari daga bakin matarsa, A'isha Buhari da 'ya'yanta mata, Dansa Namiji, Yusuf Buhari bai ce uffan ba. Iyalan tsohon shugaban kasar sun rika bayyana abubuwan da ya faru a mulkinsa a cikin wani littafi da aka rubuta na tarihin Rayuwarsa. Rahotanni sun ce, Tun yana raye, shugaba Buhari yace ba zai rubuta littafi akan tarihin Rayuwarsa ba. Wasu a ganin cewa dalili kenan da yasa Yusuf Buhari bai ce uffan ba kan rayuwar mahaifin nasa dan girmama abinda yake so.
Sanatoci sun ce in rokeka a sake duba janye musu jami’an tsaron ‘yansanda da aka yi, dan basu iya komawa garuruwansu haka ba jami’an tsaro>>Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu

Sanatoci sun ce in rokeka a sake duba janye musu jami’an tsaron ‘yansanda da aka yi, dan basu iya komawa garuruwansu haka ba jami’an tsaro>>Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu

Duk Labarai
Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cewa sanatoci sun ce ya rokeshi ya sake duba janye musu jami'an tsaron da yayi. Sanata Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu hakanne a yayin da shugaban ya je gabatar da kasafin kudin shekarar 2026a zauren majalisar. A baya dai shugaba Tinubu ya bayar da umarnin janyewa duk wani babba a kasarnan jami'an tsaron 'yansanda. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2002026911514366315?t=OqiCx2PMjD8NZBToUV1Umw&s=19
Sojojin Najeriya 11 da kasar Burkina Faso ta saki sun isa kasar Ghana

Sojojin Najeriya 11 da kasar Burkina Faso ta saki sun isa kasar Ghana

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, sojojin Najeriya guda 11 da kasar Burkina Faso ta saki tare da jirginsu C-130 sun isa kasar Ghana Rahoton yace sun samu tarba me kyau a kasar wanda hakan ke kara tabbatar da kyakkyawar alakar dake tsakanin Najeriya da kasar Ghana. Hakanan kuma a ranar Asabar ne zasu ci gaba da tafiyarsu zuwa kasar Portugal wadda dama can suka nufa suka makale a kasar Burkina Faso.
Man Fetur din Najeriya yayi kwantai a kasuwar Duniya

Man Fetur din Najeriya yayi kwantai a kasuwar Duniya

Duk Labarai
Rahotanni sun ce ganga kusan miliyan 20 na danyen man fetur din Najeriya da ake son sayarwa a tsakanin watannin Disamba zuwa January har yanzu yana nan ba'a sayar dashi ba. Kafar Reuters tace itama kasar Angola danyen man nata nacan Jibge an kasa sayar dashi. Rahoton yace kasashen biyu na ta kokarin ganin sun samu masu sayen danyen man fetur din nasu amma abu ya faskara. Rahotanni sun ce kasar China wadda tana daya daga cikin manyan masu sayen danyen man na kasashen Afrika ta fara komawa sayen man daga kasashen Larabawa saboda yafi saukin farashi da kuma saukin sufuri.