
Ministan Sufurin Jiragen sama, Festus Keyamo ya bayyana cewa, bayyana cewa, irin su shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu mutane ne na musamman ‘yan Baiwa.
Wanda yace a zamanin da irin su basa bukatar sai sun je aji kamin su samu takardar kammala Firamare ko sakandare ta GCE.
Yace daga gida suke rubuta jarabawa sai a basu takardar kammala makarantun.
Ya bayyana hakane a gidan Talabijin na Arise TV yayin da ake ganawa dashi game da maganar cece-kuce da akw na cewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bai baiwa INEC takardun kammala Firamare da sakandare ba.