Tuesday, May 19
Shadow

Wallahi sai da ka dirkawa matarka cikin shege kamin ka aureta kuma idan kace karya nake ka kaini kotu ina da hujja>>Wata Budurwa ta gayawa dan Tsohon Gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai

Takaddama ta barke tsakanin wata budurwa da dan gidan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Bashir El-Rufai a dandalin X wanda a baya ake kira da Twitter.

Budurwar dai me amfani da sunan Felexible Queen ta mayarwa da Bashir Martanine akan maganar da yayi ta shagube kan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda tace tasan Shugaba Tinubu ya baiwa ‘ya’yansa tarbiyya ba zasu fito suna cin zarafin mutane ba.

Ta jawo hankalin Tsohon gwamnan da cewa ya yiwa dan nasa magana kan abinda yake aikatawa.

Saidai lamarin ya kazance bayan da bashir ya mayar mata da martanin cewa, tana yawo otal-otal tana biyawa tsaffin mutane da suka kai sa’annin babanta bukata.

Karanta Wannan  Babbar Kotun jihar Kaduna ta sake daga sauraron bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sai zuwa watan June

Ta mayar mai da martanin cewa shi Jahili ne marar addini i da tace kawai zai yi mata kazafine amma bashi da hujja inda ta kara da cewa, “You can only slander me with no proof, jahili mara addini kawai. Da zakayi ma kanka fada bakar shaye shaye da zaifi. Ni fah zanci ubanka a duniya a lahira na samu lada kaifa saidai spendering, very normal way of winning arguments “

Maganganun sun kazance sosai inda a karshe, Flexible Queen ta bayyana cewa Bashir El-Rufai sai da yawa matarsa cikin shege kamin ya aureta.

Sannan tace idan ya isa ya kaita Kotu akan maganarnan dan kuwa tana da hujja.

Karanta Wannan  Shugaban Jami'ar Tarayya Dake Lafia Kenan, AbdulRahman Yake Sanya Hannu A Jikin Rigunan Daliban Da Suka Kammala Karatu A Jami'ar, Inda Ya Hore Su Da Su Kasance Masu Da'a A Yayin Bukukuwan Kammala Karatun

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *