Wednesday, July 8
Shadow

Kalli Bidiyon: Yanda matar tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ke rokon shugaba Tinubu, Kai Uba ne ga kowa dan Allah a sassautawa mijina sharudan beli saboda sharudan da aka saka masa yanzu ba zai iya cika su ba

Matar tsohon gwamnan Kaduna, Hajiya Asiya Nasiru El-Rufai da kishiyarta, Aichatou sun kira taron manema labarai inda a ciki suka roki shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya taimaka ya saka baki a maganar shari’ar mijinsu.

Tace babu lungu da sakon da bata shiga ba a Kaduna tawa Shugaba Tinubu yakin neman zabe sannan kuma shima mijinta ya masa yakin neman zabe.

Tace ba wai sun ce kada a hukunta mijin nasu ba amma a bashi hakkokin da doka tace a bashi na ganin likitansa da bayar da belinsa.

Tace suna neman a sassauta sharudan belin da aka gindaya masa inda tace wanda aka saka masa yanzu sun yi tsauri ba zai iya cikasu ba.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Bayan da Kungiyar Izala ta dakatar da Sheikh Alkali Zaria daga yin wa'azi, ya canja masallaci inda yaci gaba da wa'azinsa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *