Monday, January 12
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Bamu so Abinda ya faru tsakanin Kwankwaso da Ganduje ya faru da Abba>>Inji Tijjani Gandu

Bamu so Abinda ya faru tsakanin Kwankwaso da Ganduje ya faru da Abba>>Inji Tijjani Gandu

Duk Labarai
Daya daga cikin mawakan Kwankwasiyya, Tijjani Gandu ya fito ya bayyana cewa basa son Rabuwar Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da Shugaban Tafiyar Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso. Ya bayyana cewa ba wai basa son Abba ya bar NNPP bane. Amma abinda suke cewa, shine Duk inda Abba zai tafi, su tafi tare da Kwankwaso. Hakan na zuwane bayan da rade-radi suka yi yawa cewa, Abba zai koma jam'iyyar APC. Rade-radin sun kara karfi bayan da aka ga Abba ya gana da shuwagabannin jam'iyyar APC na Kano.
Kalli Bidiyon: Matashi wanda yayi ikirarin shi dan dariqa ne ya dauki hankula bayan da aka ganshi yana shan Qiya

Kalli Bidiyon: Matashi wanda yayi ikirarin shi dan dariqa ne ya dauki hankula bayan da aka ganshi yana shan Qiya

Duk Labarai
Matashi wanda yayi ikirarin cewa shi dan darikar Tijjaniyya ne ya dauki hankuka bayan da aka ganshi yana shan giya. Matasashin yace duk wanda baya darikar Tijjaniyya an barshi abaya. A cewarsa a Darikar Tijjaniyya ce kadai mutum zai sha Giya. https://www.tiktok.com/@anas_n_f_s/video/7589927983427685644?_t=ZS-92iE2ijlUTx&_r=1
Da Duminsa: Sanata Godswill Akpabio yace ya yafewa Sanata Natasha Akpoti yace lauyoyi su janye karan da ya shigar akanta

Da Duminsa: Sanata Godswill Akpabio yace ya yafewa Sanata Natasha Akpoti yace lauyoyi su janye karan da ya shigar akanta

Duk Labarai
Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya ce ya yafewa Sanata Natasha Akpoti abinda ta masa. Sannan yace ya baiwa lauyoyin sa umarnin su janye karar da ya shigar akanta dama duka wasu da ya ke kararsu akan sun bata masa suna. Yace dalilinsa na yin haka shine Faston sa ya masa wa'azi kuma wa'azin ya shigeshi. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2006714564621037783?t=d8iGOafoZPdJz0fJ7bzYbw&s=19
Allah Sarki:An samu wani ya saiwa matashiyar nan da wani yawa wayau ya tafi mata da waya sabuwar waya

Allah Sarki:An samu wani ya saiwa matashiyar nan da wani yawa wayau ya tafi mata da waya sabuwar waya

Duk Labarai
Matashiyarnan da ta ce sun hadu da wani a Shoprite Kano ya mata wayau da sunan yana sonta ya tafi mata da waya, Rahotanni sun ce an samu wani ya sai mata waya. A baya dai, Hutudole ya kawo muku yanda aka ga matashiyar na ta rusa kuka inda tace an tafi mata da waya. Da aka tambayi kudin wayar an ce Naira 95k ne. Saidai a yanzu an samu wani ya sai mata sabuwar waya.
Kalli Bidiyon: A karshe Dai Sheikh Salihu Zaria yayi bayani filla-filla kan Rahotannin dake cewa An afka masa saboda magana kan Haraji

Kalli Bidiyon: A karshe Dai Sheikh Salihu Zaria yayi bayani filla-filla kan Rahotannin dake cewa An afka masa saboda magana kan Haraji

Duk Labarai
Malamin addinin Islama, Sheikh Salihu Zaria ya yi karin haske kan Harin da ake cewa an kai masa saboda yayi magana akan Haraji. Malamin yace ba gaskiya bane, ba'a kai masa hari ba. Yace har ma Karatu yayi, dan haka masu cewa, an kai masa Hari karya suke. Yace kuma sune suka tallata gwamnatin Musulim Muslim kuma a yanzu bata abinda ya kamata dan haka dole su fito su fada. https://www.tiktok.com/@dclhausa/video/7590339768127409430?_t=ZS-92i0aHm9ROy&_r=1
Kalli Bidiyon: A akidar Ahlussunah da kuma koyarwar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) babubinda akace talakawa su dumama Shuwagabannin, kamar yanda Sheikh Salihu Zaria ke cewa>>Inji Dr. Jamilu Aliyu

Kalli Bidiyon: A akidar Ahlussunah da kuma koyarwar Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) babubinda akace talakawa su dumama Shuwagabannin, kamar yanda Sheikh Salihu Zaria ke cewa>>Inji Dr. Jamilu Aliyu

Duk Labarai
Malam Dr. Jamilu Aliyu ya bayyana cewa yana tare da Sheikh Salihu zaria game da kin biyan Haraji da gwamnati ke kokarin sakawa Talakawa Saidai yace baya tare da Malam Salihu Zaria akan cewa wai a Dumama 'yan Majalisa, yace ba koyarwa lr Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) bace dumama shuwagabanni. Yace Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yayi umarni da a yi hakuri idan aka samu shuwagabanni marasa adalci. Malam kuma yace wasa yayi yawa a wa'azin Sheikh Salihu Zaria inda yace ya kamata ya gyara. https://www.tiktok.com/@isah_bello_assalafy_garo/video/7590329793590152468?_t=ZS-92huS6g5bNp&_r=1