
Yadda ‘yan tà’àddà suka kàshè sojoji suka kwashe màkàmài a sansanin soji a Borno, Sojojin dai sun tsere yayin da màhàràn suka afkawa sansanin nasu, saidai da gari ya waye sun koma, Kalli bidiyon Yanda sojojij ke kuka, da hotunan gawarwakin wadanda aka kashe birjik a kasa
Mayaƙan Boko Haram sun kashe sojoji da ba a san adadinsu ba tare da yin awon gaba da wasu da dama bayan wani ƙazamin hari da suka kai a sansanin soji da ke yankin Marte a Jihar Borno.
Majiyoyin soji sun ce mayaƙan ƙungiyar sun fi karfin sojojin, inda suka kwashi makamai masu tarin yawa sa’annan suka cinna wa ma’ajiyar makamai da ke sansanin sojin wuta.
Mazauna yankin sun bayyana cewa da misalin ƙarfe 3 na asuba, kafin wayewar garin ranar Asabar ne Boko Haram ta ƙaddamar da harin.
https://twitter.com/SaharaReporters/status/1922035239003562473?t=NnNR7DazlyCWs6i2qrXRdA&s=19
Wani soja da ya nemi a ɓoye sunansa ya ce, “ISWÀP ta ƙwace Marte, an kashe sojoji da dama, an kama wasu, amma wasu sun samu sun tsere zuwa Dikwa, inda runduna ta 24 take.
“’Yan ta’addan sun ƙona tankok...