Monday, February 16
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon: Abinda wani Kirista yawa Sarkin Musulmi da ya sa ake ta masa Tofin Allah Tsynè

Kalli Bidiyon: Abinda wani Kirista yawa Sarkin Musulmi da ya sa ake ta masa Tofin Allah Tsynè

Duk Labarai
Wani Kirista ya wallafa Bidiyon me Alfarma Sarkin Musulmi da ya kirkira da AI wanda yake nuna cewa shi Kirista ne. Bidiyon ya jawo cece-kuce da Allah wadai sosai inda mutane ke ta kiran ya kamata a kamashi. Kiristan na zaunene a kasar Italiya, wasu sun ce sun aikawa hukumomin kasar Italiya da korafi akansa dan a hukuntashi. https://twitter.com/i/status/2009330648725717266 https://twitter.com/i/status/2009334310743236648
Dan kasar Dr. Congo, Lumumba VEA wanda ya ruka tsayawa kyam har sai an gama wasa an masa tayin dala $2000 duk wasa ya zama jakadan AFCON amma yaki ya ya koma goda da tawagar kasarsa

Dan kasar Dr. Congo, Lumumba VEA wanda ya ruka tsayawa kyam har sai an gama wasa an masa tayin dala $2000 duk wasa ya zama jakadan AFCON amma yaki ya ya koma goda da tawagar kasarsa

Duk Labarai
Dan kasar Dr. Congo, Lumumba VEA wanda ya rika tsayawa kyam kamar Gunki a duk sanda ake wasa da kasarsa an masa tayin ya tsaya a kasar Morocco ya zama jakadan AFCON amma yaki. An masa tayin za'a rika bashi dala $2000 duk wasa amma yaki amincewa ya koma gida da tawagarsa ta kasar Dr. Congo din bayan an ciresu daga gasar AFCON.
Kalli Bidiyon Da Duminsu: Yanda Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami ya koma gida a jirgin sama shi da dansa da matarsa bayan da aka bayar da belinsu

Kalli Bidiyon Da Duminsu: Yanda Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami ya koma gida a jirgin sama shi da dansa da matarsa bayan da aka bayar da belinsu

Duk Labarai
Tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami kenan a wannan Bidiyon tare da Dansa da matarsa suka koma gida a jirgin sama bayan da aka bayar da belinsu. An ga mutane sun musu tarba ta karamchi ana ta tafi. EFCC dai na zargin Malami da satar sama da Naira 8 sannan ta kwace kadarorinsa har guda 57 wanda darajarsu ta haura Naira Biliyan 200. Kotu dai ta bayar da belin malami da dansa da matarsa akan Naira Miliyan 500 bayan sun sha zama a gidan yarin Kuje. https://twitter.com/i/status/2009513897754083484
Allah Sarki: Duk da Kotu ta bayar da belinsa, ji dalilin da yasa tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami ya zabi ya ci gaba da zama a gidan yari

Allah Sarki: Duk da Kotu ta bayar da belinsa, ji dalilin da yasa tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami ya zabi ya ci gaba da zama a gidan yari

Duk Labarai
Rahotanni sun ce tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami na jan kafa wannan kokarin samun beli ya fito daga gidaj yarin kuje. Kotun tarayya dakw Abuja ta bayar da belinsa dana matarsa. Saidai Rahotanni sun ce jami'an DSS kusan 50 sun je gidan yarin suna jiran a bayar da belin sa su sake kamashi. Dalili kenan ma da yasa Abubakar Malami ke jan kafa wajan cika shariddan Belin dan a sakeshi Rahotanni dai sun ce dan Abubakar Malami wanda ake tsare dasu tare na can a Asibitin gidan yarin bayan da rashin lafiya ta sameshi tun ranar farko da aka kaisu gidan yarin
Allah Sarki: Kaptin din Najeriya, Wilfred Ndidi yace kungiyar kwallon kafa ta Najeriya, Super Eagles su ci gaba da Atisaye kawai, Idan Gwamnati bata biyasu hakkinsu ba shi zai biya

Allah Sarki: Kaptin din Najeriya, Wilfred Ndidi yace kungiyar kwallon kafa ta Najeriya, Super Eagles su ci gaba da Atisaye kawai, Idan Gwamnati bata biyasu hakkinsu ba shi zai biya

Duk Labarai
Kaftin din kungiyar kwallon kafa ta Najeriya, Wilfred Ndidi ya ce a ci gaba da atisaye dan shirin wasan Najeriya da Algeria. Inda yayi Alkawarin idan Gwamnatin Najeriya bata biya hakkokin 'yan kwallon ba nan da ranar Asabar, shi zai biya. 'Yan kwallon na super Eagles dai sun ce ba zasu yi Atisaye ba sai an biyasu hakkokin wasannin baya da suke bi. Gwamnatin tarayya tuni tace an kammala komai na biyan 'yan wasan hakkokinsu inda tace a yau Alhamis zuwa gobe 'yan kwallon zasu fara jin Alert na hakkokin nasu. Da yawa dai sun bayyana wannan lamari da abin Kunya.
Kungiyar Ma’aikata Gidajen man fetur sun ce basu yadda da sabon gidan man A A Rano wanda babu masu matsa mai ba, me abin hawa da kansa zai rika zuba mansa

Kungiyar Ma’aikata Gidajen man fetur sun ce basu yadda da sabon gidan man A A Rano wanda babu masu matsa mai ba, me abin hawa da kansa zai rika zuba mansa

Duk Labarai
Kungiyar ma'aikatan gidajen mai sun yi Allah wadai da sabunta gidajen man A A Rano ke shirin yi inda yake son kawo tsari irin nankasashen Turai wanda babu me matsa mai saidai me abin hawa ne da kansa zai rika zuba man da kansa. Sannan gidajen man zasu rika aiki tsawon awanni 24, ma'ana duk tsakar dare mutum zai iya zuwa ya tarar da man fetur ya sha. Kungiyar ta ma'aikatan gidan man tace idan aka tabbatar da wannan tsarin, zai sa membobinta su rasa ayyukan yi.