Thursday, March 26
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kotu Ta daure Tsohon Akanta janar na Najeriya Chukwunyere Anamekwe Nwabuoku tsawon shekaru 72 saboda satar Naira Miliyan N868.4

Kotu Ta daure Tsohon Akanta janar na Najeriya Chukwunyere Anamekwe Nwabuoku tsawon shekaru 72 saboda satar Naira Miliyan N868.4

Duk Labarai
Babbar kotun tarayya dake Abuja ta daure tsohon Akanta Janar na kasa, Chukwunyere Anamekwe Nwabuoku bayan samunsa da laifin satar kudade da suka kai Naira Miliyan N868.4 Mai shari'a, Justice James Omotosho ne ya yanke masa hukuncin ranar Litinin bayan gamsuwa da hujjojin da aka gabatar masa kan zargin. An zargeshi da saka kudi a wasu asusun bankunan kamfanoni 4 wanda a baya ya karyata yace bai ma taba jin sunayen kamfanonin ba. Saidai daga baya ya amsa cewa lallai ya tura kudade zuwa asusun ajiyar kudi na wadannan kamfanonin. Kamfanonin sune kamar haka: Temeeo Synergy Concept Limited, Turge Global Investment Limited, Laptev Bridge, sai kuma Arafura Transnational Afro Limited. Chukwunyere Anamekwe Nwabuoku a yanzu dai shekarunsa 64 a Duniya.
Da Duminsa: DSS sun sake kai samame gidan Tsohon Ministan shari’a Abubakar Malami

Da Duminsa: DSS sun sake kai samame gidan Tsohon Ministan shari’a Abubakar Malami

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, DSS sun sake kai samame gidan tsohon Ministan shari'a Abubakar Malami a yau, Litinin. Samamen na DSS na zuwa jim kadan bayan da tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya kaiwa Abubakar Malami ziyara gidan nasa. Rahotanni wanda Sahara Reporters ta ruwaito, tace DSS sun zagaye gidan na Malami yayin da Atiku ya kai masa ziyara, kuma bayan da Atikun ya tafi ne sai suka afka cikin gidan suka kori kowa daga ciki. Hakan na zuwane dai yayin da ake zargin gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da yunkurin murkushe 'yan Adawa kamin zaben shekarar 2027.
Da Duminsa: A karshe dai ICPC ta saka ranar da zata Gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai a gaban kotun Gwamnatin tarayya

Da Duminsa: A karshe dai ICPC ta saka ranar da zata Gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai a gaban kotun Gwamnatin tarayya

Duk Labarai
Hukumar yaki da rashawa ta ICPC ta bayyana cewa ta shirya tsaf dan gurfanar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a gaban babbar kotun tarayya dake Kaduna. Hukumar tace za'a gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai ne bisa zargin Almundahanar kudade, damfara da kuma amfani da ofishinsa ta hanyar da bata dace ba. Sanarwar tace za'a gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai ne tare da wani me suna  Joel Adoga ranar 24 ga watan Maris. Hakanan sanarwar tace akwai shari'a ta daban itama da za'a shigar da tsohon gwamnan Kadunan a babbar kotun jihar kaduna itama inda ake zarginsa da aikata ba daidai ba da ofishinsa da kuma karkatar da kudade.
Kalli Bidiyon: Idan ba zaki yiwa mijinki wanki da Guga ba, to baki shirya zama a gidan Aure ba>>Inji Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah

Kalli Bidiyon: Idan ba zaki yiwa mijinki wanki da Guga ba, to baki shirya zama a gidan Aure ba>>Inji Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah

Duk Labarai
Malam Abdulrahman Umar Sautussunnah ya bayyanawa mata cewa idan ba su shirya yiwa mijinsu wanki da guga ba to basu shirya yin zaman aure ba. Malam ya bayyana hakane a wajan wani karatunsa inda yace ba wai yana gayawa maza su rika saka matansu wanki da guga bane, yana gayawa mata irin nauyin hakkin mazajensu dake kansu. https://www.tiktok.com/@abdurrahmanumarr/video/7620038430436789525?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7620038430436789525&source=h5_m&timestamp=1774257847&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_med...
Kalli Bidiyon: Matashi ya dauki hankula saboda yanda yanda yake ta nuna wayarsa ta iPhone yayin da ake hira da malaminsa

Kalli Bidiyon: Matashi ya dauki hankula saboda yanda yanda yake ta nuna wayarsa ta iPhone yayin da ake hira da malaminsa

Duk Labarai
Wannan wani matashi ne da ya dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da aka ga yana ta kokarin nuna wayarsa ta iPhone yayin da ake hira da malaminsa. Matashin ya rika ciro wayar daga Aljihunsa yana jujjuyata a hannunsa inda lamarin ya dauki hankula sosai ake ta bayyana mabanbanta ra'ayoyi akai. https://www.tiktok.com/@gwamnan.bunaye/video/7598936358530452754?_r=1&_t=ZS-94vKMEeBC88&sp_source=7537614245375297080
Kayan Masarufi zasu yi tsafmda kuma Talauci zai karu, Inji Shugaba Tinubu

Kayan Masarufi zasu yi tsafmda kuma Talauci zai karu, Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi gargadin cewa rikicin gabas ta tsakiya zai iya shafar Najeriya ta hanyar da kayan masarufi zasu yi tsada sannan karancin kudi a hannun mutane zai yi kamari. Shugaban ya bayyana hakane a Legas yayin da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima da wasu gwamnoni 23 suka je masa gaisuwar Sallah. Shugaban yace zuwansa Ingila abinda suka fi baiwa muhimmanci shine hadaka da samarwa Najeriya kayan aiki dan magance matsalar tsaro. Shugaba Tinubu yace ya kuma yi magana da shugaban kasar Faransa shima yayi alkawarin baiwa Najeriya kayan aiki dan magance matsalar a tsaro. Yace kuma yana nan yana kara tuntubar sauran wasu shuwagabannin.
Kalli Bidiyon: Idan kuna da wanda ya zamar muku ala kakai, Qadangaren Bakin Tulu, Wanda kuke ga kamar ba za’a iya tureshi ba to ku dage da Addu’a>>Inji Sheikh Mansur Yelwa

Kalli Bidiyon: Idan kuna da wanda ya zamar muku ala kakai, Qadangaren Bakin Tulu, Wanda kuke ga kamar ba za’a iya tureshi ba to ku dage da Addu’a>>Inji Sheikh Mansur Yelwa

Duk Labarai
Sheikh Mansur Isa Yelwa ya bayyana cewa idan akwai wanda mutane suke ganin ya zamar musu Alakakai, wanda suke ganin kamar ba za'a iya Tureshi ba. Yace wanda ake ganin ya shirya, yace to mutane su tashi a yi ta addu' da gaske. Yace ko dai ya sauka da kansa, ko kuma Allah ya saukeshi, yace kuma Allah zai saukeshine ba a doron kasa ba, a kabari. https://twitter.com/i/status/2035842882297356391