Monday, February 16
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Da Duminsa: Bayan da suka Haramtawa ‘yan kasar Amurka shiga kasarsu, Kasar Mali ta kama wani dan Amurka ya shiga kasarta

Da Duminsa: Bayan da suka Haramtawa ‘yan kasar Amurka shiga kasarsu, Kasar Mali ta kama wani dan Amurka ya shiga kasarta

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Mali na cewa, kasar ta kama wani dan kasar Amurka da ya shigar mata kasa. Tuni kuma aka mayar dashi kasarsa. Kasar Mali dai ta hana 'yan kasar Amurka shigar mata kasa a matsayin martani ga hanin da kasar ta Amirka tawa 'yan kasar Mali shigar mata kasa. https://twitter.com/i/status/2008230251382309256
Ji abinda Kwankwaso yace akan Abba game da zagayowar ranar Haihuwar gwamnan Kanon

Ji abinda Kwankwaso yace akan Abba game da zagayowar ranar Haihuwar gwamnan Kanon

Duk Labarai
Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya taya Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf murnar zagayowar ranar Haihuwarsa. Ya wallafa sako a shafinsa na X inda yace yana Taya Abba Murnar zagayowar ranar Haihuwarsa. Kwankwaso yace ya tuna irin yanda suna yi rayuwa tare da Abba inda ya masa mataimaki na musamman a lokacin yana Gwamna a zangon farko, hakanan sanda ya zama Ministan tsaro ya kuma tafi da abba a matsayin mataimaki na musamman. Kwankwaso yace bayan nan ma kuma daya sake zama Gwamnan Kano, ya sake dauko abba a matsayin kwamishina kamin daga baya ya zama gwamnan Kano. Kwankwaso yace sun yi aiki tare dan ciyar da jihar Kano gaba. inda yace yana masa fatan Alheri. https://twitter.com/i/status/2008306292075421909
Allah Sarki: Na karanta Qur’ani na fahimci cewa wannan littafi ne da ba wani mutum da ya isa ya Rubutashi, Shiyasa ni da matata muka musulunta>>Inji Baturen Ingila, Dr. Mark Thompson

Allah Sarki: Na karanta Qur’ani na fahimci cewa wannan littafi ne da ba wani mutum da ya isa ya Rubutashi, Shiyasa ni da matata muka musulunta>>Inji Baturen Ingila, Dr. Mark Thompson

Duk Labarai
Baturen Ingila, Dr. Mark Thompson wanda yanzu ya canja suna zuwa Abdullahi ya karbi Musulunci shi da matarsa. Yace ya karanta Qur'ani ya fahimci cewa Littafi ne wanda mutum bai isa ya rubutashi ba dan haka shi da matarsa suka karbi Musulunci. Yace ya ziyarci Makkah yayi ibada amma kuma da ya koma kasarsa, sai ya kasa samun nutsuwa. Yace dan hakane ya sake komawa dan yayi Ibada.
Kalli Bidiyon: Rikicin Osimhen da Ademola Lukman ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Rikicin Osimhen da Ademola Lukman ya dauki hankula

Duk Labarai
A wasan da Najeriya ta buga da Mozambique a daren jiya, An ga Victor Osimhen nawa Ademola Lukman tsawa a filin wasan. Lukman dai be biye masa ba wanda hakan yasa wasu suka rika sukar Osimhen game da lamarin. https://twitter.com/i/status/2008282216510447942 Bayan wasan an tambayi Ademola Lukman kan cewa menene ya faru tsakaninsa da Victor Osimhen, saidai ya kayar da baki yace ba komai wasane. https://twitter.com/i/status/2008312453608689986 Wannan amsa ds ya bayar ta dauki hankulan mutane sosai inda akai ta yaba masa.
Duk wani Ahlussunah farin ciki ya kamata yayi da kamun da akawa Sheikh Khalifa Sani Zaria>>Inji Dr. Hussain Kano

Duk wani Ahlussunah farin ciki ya kamata yayi da kamun da akawa Sheikh Khalifa Sani Zaria>>Inji Dr. Hussain Kano

Duk Labarai
Dr. Hussain Kano ya bayyana cewa, duk wani Ahlussunah kamata yayi ace yayi farin ciki da kama Sheikh Khalifa Sani Zaria. Ya bayyana cewa dalili shi dan bidi'a ne. Yace idan Abu ya samu dan Bidi'a farin ciki ake amma idan ya samu Musulmi me sabo, shi kuma jaje ake mada. https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7592008808231210252?_t=ZS-92pW4UzN2e1&_r=1
Kalli Bidiyon: Sheikh Khalifa Sani Zaria, Matsafine>>Inji Baffa Hotoro

Kalli Bidiyon: Sheikh Khalifa Sani Zaria, Matsafine>>Inji Baffa Hotoro

Duk Labarai
Baffa Hotoro ya bayyana Sheikh Khalifa Sani Zaria da jami'an tsaro suka kama da cewa matsafi ne boka. Ya bayyana hakane a martanin da yake kan zargin cewa an baiwa Malam Sheikh Khalifa Sani Zaria kudi yayi addu'a. Ya bayyana cewa dama Allah ba zai karbi irin wannan Addu'a ba dan kuwa dan kudi aka yi ta. https://www.tiktok.com/@zaidou1taza/video/7592001048626220344?_t=ZS-92pUvfB3gRN&_r=1