Monday, February 16
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Da Duminsa: Manchester United ta kori Ruben Amorim a matsayin kocinta

Da Duminsa: Manchester United ta kori Ruben Amorim a matsayin kocinta

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kungiyar Manchester United ta kori Ruben Amorim a matsayin kocinta. Hakan na zuwane bayan da ya kwashe watanni 14 yana matsayin kocin Kungiyar. Dangantaka ta yi tsami tsakanin dan kasar Portugal din me shekaru 40 da kungiyar a 'yan kwanakinnan. Manchester United dai a yanzu tana matsayi na 6 akan teburin Premier league. Manchester United ta sanar da Darren Fletcher a matsayin kocin wucin gadi.
Kudaden Bashin da Shugaba Tinubu ke karbowa da ‘yan Najeriya yake baiwa su yi Jari da an samu saukin Rayuwa>>Inji Peter Obi

Kudaden Bashin da Shugaba Tinubu ke karbowa da ‘yan Najeriya yake baiwa su yi Jari da an samu saukin Rayuwa>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party a zaben shekarar 2023 data gabata, Peter Obi ya bayyana cewa, kudaden da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ke karbowa Bashi, da Tallafawa 'yan Najeriya yake yi da jari da ba haka ba. Yace ana ta cewa babu kudi amma kuma gwamnati na ta kara ciwo bashi. Ya ce wadanda aka baiwa su yi jari zasu samarwa wasu aikin yi ta hakane za'a samu saukin talaucin da ake fama dashi a kasarnan. https://twitter.com/i/status/2007903277632069826
Da Duminsa: Fadar Shugaban kasa ta yi magana kan abin kunyar da ake zargin shugaba Tinubu da yi

Da Duminsa: Fadar Shugaban kasa ta yi magana kan abin kunyar da ake zargin shugaba Tinubu da yi

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta yi martani kan abin kinyar da ake zargin shugaban da yi ta hanyar wallafa Hoton AI a shafinsa na X. Me magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya bayyana cewa, Hoton bana AI bane. Yace da gaske shugaba Tinubu da Takwaransa, Paul Kagame suna kasar Faransa kuma sun gana. Yace wanda ya daukesu hotonne wayarsa bata daukar hoto me kyau shine yayi Amfani da AI ya gyara hoton. Lamarin hoton dai ya jawo cece-kuce sosai a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/i/status/2008092644266656148
Kalli Bidiyon:Daga yau na bar Darikar Tijjaniyya tunda daga ‘yan Damfara sai wanda ake baiwa kudi su nemo Bokaye a cikinta>>Inji Anas

Kalli Bidiyon:Daga yau na bar Darikar Tijjaniyya tunda daga ‘yan Damfara sai wanda ake baiwa kudi su nemo Bokaye a cikinta>>Inji Anas

Duk Labarai
Wani matashi me suna Anas ya bayyana cewa, daga yau ya bar Darikar Tijjaniyya. Matashin ya bayyana hakane a shafinsa na Tiktok inda yace yaga daga masu kudin Karya sai 'yan Damfara sai wanda ake baiwa kudi su samo bokaye. https://www.tiktok.com/@anas_n_f_s/video/7591556066911997195?_t=ZS-92oV1d42bI1&_r=1
Kalli Bidiyon: An bayyana abinda Kasar Amùŕkà zatawa Shugaba Tinubu idan aka yi magudin zabe a 2027

Kalli Bidiyon: An bayyana abinda Kasar Amùŕkà zatawa Shugaba Tinubu idan aka yi magudin zabe a 2027

Duk Labarai
Dan PDP, Dr. Adetukunbo Pearse ya bayyana cewa idan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yayi magudin zabe a zaben shekarar 2027 Zai bace. Ya bayyana cewa, idan hakan ta faru Shugaban kasar Amurka zai dauke Shugaba Tinubu kaar yanda yayiwa shugaban kasar Venezuela. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan Talabijin na Channels TV. https://twitter.com/i/status/2007837051249741877
Shugaba Tinubu na sha zazzafar suka saboda wani abu da yayi da ya jawowa Najeriya abin magana

Shugaba Tinubu na sha zazzafar suka saboda wani abu da yayi da ya jawowa Najeriya abin magana

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na shan suka saboda wallafa hoton da ake zargin an yishi da AI(watau hoton Boge) Shugaban ya wallafa hotonne ta shafinsa na X. Ya wallafa cewa yana tare da shugaban kasar Rwanda, Paul Kagame inda aka gansu tare zaune. Saidai an gano cewa hoton da AI aka yishi. Hakan ya jawowa shugaban kasar suka sosai inda da yawa suka ce hakan abin kunyane ga Najeriya. https://twitter.com/i/status/2007850631579529506 https://twitter.com/i/status/2007941035385909582 https://twitter.com/i/status/2008038389296021750