Tsohon Ministan shari'a, Abubakar malami da yanzu haka ke tsare a hannun hukumar EFCC an ga Bidiyon sa da yakewa Shugaba Tinubu yakin neman zabe a shekarar 2022.
Da yawa dai cikin mabiyansa na ganin kamen da aka mai yanzu ba'a masa halacci ba.
https://twitter.com/Pharmacio001/status/2001928421698605416?t=SeCUmujj0b4lPDSp1X5KxQ&s=19
Rahotanni sun ce ganga kusan miliyan 20 na danyen man fetur din Najeriya da ake son sayarwa a tsakanin watannin Disamba zuwa January har yanzu yana nan ba'a sayar dashi ba.
Kafar Reuters tace itama kasar Angola danyen man nata nacan Jibge an kasa sayar dashi.
Rahoton yace kasashen biyu na ta kokarin ganin sun samu masu sayen danyen man fetur din nasu amma abu ya faskara.
Rahotanni sun ce kasar China wadda tana daya daga cikin manyan masu sayen danyen man na kasashen Afrika ta fara komawa sayen man daga kasashen Larabawa saboda yafi saukin farashi da kuma saukin sufuri.
Rahotanni sun bayyana cewa farashin Gwamnati a kasuwar chanji ayau shine ana sayen dala akan farashin Naira N1,455.98.
Sanan a kasuwar bayan fage kuwa ana sayen dalar akan Naira N1,720 inda ake sayar da ita akan farashin Naira N1,745
Rahoton yace Naira ta da fadi a kasuwar ta chanji.
Rahotanni sun bayyana cewa, sojan da ya jagoranci juyin mulkin da bai yi nasara ba a kasar Benin Republic, Pascal Tigri yanzu haka yana zaune a kasar Nijar.
Rahoton yace Pascal Tigri ya samu mafakar siyasa a kasar ta Nijar inda yanzu haka yake zaune a wani gidan gwamnati dake kusa da fadar shugaban kasar Nijar.
Rahoton yace yanzu haka ana zargin kasar ta Nijar da hannu ko da ba kai tsaye bane a yunkurin juyin Mulkin.
Pascal Tigri da farko ya tsallaka zuwa kasar Togo ne inda daga nan ya hau jirgi zuwa Burkina Faso. Daga baya kuma ya sake hawa jirgi zuwa kasar Nijar.
Najeriya dai ta taimakawa kasar ta Benin Republic aka murkushe yunkurin juyin mulkin.
Sanata Godswill Akpabio ya bayyana cewa, a lokacin da ya zama kakakin majalisar Dattijai, akwai sanatoci kusan 50 a jam'iyyun adawa.
Yace amma yanzu wanda ke jam'iyyar adawa basu wuce 4 zuwa 5 ba.
Yace suma sai rokonsa suke ya kaisu wajan shugaban kasa su koma APC.
https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2001970822454591647?t=WxAMejfKUrJ0YdoZOAuxJg&s=19
Rahotanni daga babban birnin tarayya, Abuja na cewa, hukumar birnin ta fara karbar haraji daga hannun masu amfani da janareta saboda damun mutane da kararsa ke yi.
Hakan na zuwane mutane ke kukan rashun wutar Lantarki da kuma matsin rayuwa da suka fada cikin.
An ga takardar karbar irin wannan haraji na ta yawo a kafafen sada zumunta inda da yawa ke ta mamaki.
Jami'in Hukumar 'yansandan kasar Ghana, (ACP), Dennis Fiakpui yace takura a aure da saka damuwa babban laifine a kasar.
Yace a tsakanin ma'aurata, duk wanda ya hana dan uwansa ma'amalar aure, misali mace ta ki yadda da mijinta a gado, idan ya kai kara kuma kotu ta samu matar da laifi, zata fuskanci hukuncin daurin shekaru 2 a gidan yari.
Yace hakanan itama idan macence mijinta baya kwanciyar aure da ita, zata iya kaishi kara a nema mata hakkinta.
Yace hakanan idan miji na dadewa a waje baya komawa gida da wuri ko kuma ya daina cin abincin matarsa, duka zata iya kaishi kara a bi mata hakkinta.
Diyar tsohon shugaban kasa, Halima Buhari ta bayyana cewa, Mahaifinsu yana sane da cewa, mutane da yawa basu ji dadin mulkinsa ba kuma sun rika sukarsa.
Ta bayyana hakane bayan wallafa littafi akan tarihin rayuwar tsohon shugaban kasar.
Tace duk da yake akwai wanda suka godewa shugaban kasar saboda irin yanda rayuwarsu ta canja, amma tabbas akwai da yawa wanda basu dadin mulkin mahaifin nata ba.
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya yi raddi ga wasu hotunan Samha M. Inuwa dake ta yawo a kafafen sada zumunta inda aka ganta babu Make-Up ko Filter kamar yanda aka saba gani a baya.
A Bidiyon daya wallafa na kare Samha M. Inuwa, Gfresh yace wannan baba Tambaya ce ba Samha M. Inuwa ba.
Yace shima an rika yada irin wadannan hotunan nasa na karya.
https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7585239692669472007?_r=1&_t=ZS-92Lj7DN2bAG