Thursday, January 15
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Da Duminsa: Kotu taki amincewa da bayar da belin Tsohon Minista, Abubakar malami inda tace EFCC ta ci gaba da tsareshi

Da Duminsa: Kotu taki amincewa da bayar da belin Tsohon Minista, Abubakar malami inda tace EFCC ta ci gaba da tsareshi

Duk Labarai
Babbar Kotun tarayya dake Abuja ta ki amincewa da bayar da Belin tsohon Ministan shari'a, Abubakar malami inda yake neman a sakeshi daga komar EFCC. Saidai kotu a zamanta na ranar Alhamis tace EFCC ta ci gaba da tsare Malami inda Mai Shari'a, Babangida Hassan yace ci gaba da tsare Abubakar Malami bai sabawa doka ba.
Kalli Bidiyon yanda daya daga cikin sojojin Najeriya da kasar Burkina Faso ta kama ya tabbatar da cewa jirgin su tangarda ya samu shiyasa suka sauka a kasar

Kalli Bidiyon yanda daya daga cikin sojojin Najeriya da kasar Burkina Faso ta kama ya tabbatar da cewa jirgin su tangarda ya samu shiyasa suka sauka a kasar

Duk Labarai
Daya daga cikin sojoji 11 da kasar Burkina Faso ta kama tsawon kwanaki 9 bayan da jirginsu ya sauka a kasar yace, jirgin nasu da gaske tangarda ya samu. Ya bayyana hakane yayin ganawarsa da wakilan Najeriya ta tura kasar dan a baiwa shugaban kasar, Ibrahim Traore hakuri ya sakesu. Ministan harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar ne ya jagoranci tawagar. https://twitter.com/NigAffairs/status/2001594423025471848?t=_6oHc1fOg4wScDRR8smDVA&s=19
Kalli Bidiyon: Yanda aka tarbi Rahama Saidu a filin Jirgi bayan da ta dawo daga Umrah inda ta kai ‘yan uwanta

Kalli Bidiyon: Yanda aka tarbi Rahama Saidu a filin Jirgi bayan da ta dawo daga Umrah inda ta kai ‘yan uwanta

Duk Labarai
An ga yanda Tauraruwar Tiktok, Rahama Saidu ta dawo Najeriya daga kasar Saudiyya bayan da ta kai 'yan uwanta aikin Umrah. Rahama Saidu dai ta dauki hankula sosai bayan da aka ga yanda ta kai 'yan uwanta duka aikin Umrah ind akaita tsegumin ina ta samu kudin. https://www.tiktok.com/@ejarrx__cut/video/7584833334677638408?_t=ZS-92K0XvLs59F&_r=1
Hadisi ya tabbatar da cewa, Ceton Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) akan masu aikata manyan zunubaine, shiyasa nace ina son in shiga Aljannah ba da ceton Annabi ba>>Dr. Hussain Kano

Hadisi ya tabbatar da cewa, Ceton Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) akan masu aikata manyan zunubaine, shiyasa nace ina son in shiga Aljannah ba da ceton Annabi ba>>Dr. Hussain Kano

Duk Labarai
Dr. Hussain Kano wanda ya jawo cece-kuce bayan daya roki Allah yasa kada ya kai matsayin da sai Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) a ceceshi kamin ya shiga Aljannah, yayi karin Haske. Yace akwai ingantaccen Hadisi da yace Ceton Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) akan masu aikata manyan zunubaine. Yace dalilinsa kenan na fadar haka kuma su baffa Hotoro da suka masa raddi sun san da Hadisin, dan haka yace bai yafe raddin da suka masa ba kuma sai sun gani kamin su Mutu. https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7584966011799997707?_t=ZS-92Jz27DGyAr&_r=1
Kalli Hotunan Ministan harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar da sojojin Najeriya 11 da kasar Burkina Faso ta tsare inda ya tabbatar da an sakesu

Kalli Hotunan Ministan harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar da sojojin Najeriya 11 da kasar Burkina Faso ta tsare inda ya tabbatar da an sakesu

Duk Labarai
Ministan harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar ya tabbatar da sakin Sojojin Najeriya 11 da kasar Burkina Faso ta kama. An ganshi da sojojin inda suka dauki hotuna tare. Ya bayyana cewa, Najeriya tafi baiwa sulhu Muhimmanci a wajan warware matsaloli a yankin Afrika ta yamma. Sannan kuma yafe sun tattauna karfafa alaka me kyau tsakanin Najeriya da kasar Burkina Faso. https://twitter.com/YusufTuggar/status/2001557495089619258?t=HyqzNjHjtsfH1uc2d5QWIw&s=19
Kalli Bidiyon Allah Sarki: Shekara daya kenan da daukar Bidiyon a yayin da ake taya tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari murnar cika shekaru 82 a Duniya

Kalli Bidiyon Allah Sarki: Shekara daya kenan da daukar Bidiyon a yayin da ake taya tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari murnar cika shekaru 82 a Duniya

Duk Labarai
Wannan Bidiyon yanda aka taya tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari kenan murnar cika shekaru 82 a Duniya shekarar data gabata. Hadimin shugaban kasar, Bashir Ahmad ne ya bayyana haka inda yace a wancan lokacin babu wanda yayi tunanun shugaba Buhari zai rasu. https://www.tiktok.com/@bashirahmaad/video/7584973051096337682?_t=ZS-92Jsp2ZjZPk&_r=1
Kalli Bidiyo: Masu mana sharrin zhaghin Sahabbai su kuma Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) suke zagi>>Inji Sheikh Zakzaky

Kalli Bidiyo: Masu mana sharrin zhaghin Sahabbai su kuma Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) suke zagi>>Inji Sheikh Zakzaky

Duk Labarai
Sheikh Ibrahim Zakzaky ya bayyana cewa, masu musu sharrin suna zagin Sahabbai su kuma Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) suke zagi. Ya bayyana cewa to a tsakanin su wa yafi girman laifi? Ya kuma nemi ma a kawo masa inda suke zagin sahabban. https://www.tiktok.com/@real_dadson/video/7584598762299952405?_t=ZS-92Jp3GlB68n&_r=1
Kalli Bidiyon: Toh Kiristoci ‘yan uwana, da kuke ganin America na sonku gashinan ta saka dokar hana ‘yan Najeriya zuwa kasar ta amma bata ware Kiristoci ba>>Inji ‘Yar Tanko

Kalli Bidiyon: Toh Kiristoci ‘yan uwana, da kuke ganin America na sonku gashinan ta saka dokar hana ‘yan Najeriya zuwa kasar ta amma bata ware Kiristoci ba>>Inji ‘Yar Tanko

Duk Labarai
Wata Kirista me suna 'yar Tanko ta bayyanawa Kiristocin Najeriya cewa ya kamata su shiga Taitayinsu. Ta bayyana hakane a wani Bidiyo inda take martani ga dokar hana shiga Amurkar da aka kakabawa 'yan Najeriya, tace gashinan da aka tashi saka wannan doka ba'a ware Kiristoci ba. Tace dan haka yaudarar kaine tunanin Amurka tana son Kiristoci. https://www.tiktok.com/@yartanko/video/7584973349965663504?_t=ZS-92JmDZDrYMj&_r=1