Ji Dalilai huɗu da suka sa Dangote ya rage farashin man fetur
"Duk shikashika da za su jawo rage farashin man fetur an cika su a yanzu," kamar yadda Farfesa Ahmed Adamu - masanin tattalin arzikin man fetur a jami'ar Nile University da ke Abuja - ya shaida wa BBC.
Gasa
Tun bayan sauye-sauyen da aka samu a kasuwar hada-hadar man fetur ta Najeriya, aka fara samun gasa tsakanin masu shigo da man da kuma matatar Dangote.
Wannan gasa na ɗaya daga cikin dalilan da suka jawo raguwar farashin, ko kuma sanadiyyar hana farashin ya ƙaru.
"Da ma amfanin gasa kenan. Shi Dangote yana ganin yanzu yana yin takara ne da wasu matatun man fetur ɗin na duniya, kuma babban burinsa shi ne ya riga kowa sayarwa," in ji Farfesa Ahmed.
"Da zai yiwu ma, zai so ya haddasa yadda za a yi wasu 'yankasuwar ma su ji ba za su iya ci gaba da harkar ba, ta yadda duk masu ...







