Saturday, July 11
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Bayan da ta zargeni da nemanta da lalata Har Hotunan Selfie Sanata Natasha Akpoti ke daukar mu ni da ita idan mun tafi aiki, saboda tsabar jin dadin aiki dani kuma nace ta kawo hujjar zargin da take min amma taki

Bayan da ta zargeni da nemanta da lalata Har Hotunan Selfie Sanata Natasha Akpoti ke daukar mu ni da ita idan mun tafi aiki, saboda tsabar jin dadin aiki dani kuma nace ta kawo hujjar zargin da take min amma taki

Duk Labarai
Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya bayyana cewa, Abin mamaki bayan da sanata Natasha Akpoti ta zargeshi da cewa ya nemeta da lalata, sun yi tafiye-tafiye tare har zuwa kasashen waje aiki. Yace kuma har hotuna Selfie take daukarsu idan suna aiki saboda jin dadin aiki dashi. Yace amma kuma ya nemi ta gabatar da hujjar zargin da take masa amma taki. Sanata Natasha Akpoti dai tace ba zata bayar da hujjojin zargin da takewa, Sanata Godswill Akpabio ba sai an je kotu.
Kalli Bidiyo: Iyayen mu da suka rika haihuwar ‘ya’ya talatin akwai saukin rayuwa a lokacin amma yanzu Rayuwa ta canja dole mutum ya kula da yawan ‘ya’yan da zai haifa>>Sheikh Ibrahim Maqari

Kalli Bidiyo: Iyayen mu da suka rika haihuwar ‘ya’ya talatin akwai saukin rayuwa a lokacin amma yanzu Rayuwa ta canja dole mutum ya kula da yawan ‘ya’yan da zai haifa>>Sheikh Ibrahim Maqari

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Ibrahim Maqari ya jawo hankalin mutane akan tara 'ya'ya. Yace a baya mutane na haihuwar 'ya'ya talatin saboda akwai wadatar gurin zama kuma a wancan lokacin ba sai an saka yaro a makaranta ba. Yace amma yanzu Rayuwa ta canja, irin wancan abin ba zai yiyu ba. https://www.tiktok.com/@prof.ibrahim.maqa92/video/7500248373430078725?_t=ZM-8wB1sZ5f0AZ&_r=1 Saidai malam yace irin mutanen mu na da wahalar canjawa akan wani abu da suka saba dashi.
Cikin Girmamawa Muna Jajantawa Atiku Abubakar, Dangote, Sanata Saraki Da Dino Melaye Kan Rashin Nasarar Da Arsenal Ta Yi Akan PSG A Daren jiya

Cikin Girmamawa Muna Jajantawa Atiku Abubakar, Dangote, Sanata Saraki Da Dino Melaye Kan Rashin Nasarar Da Arsenal Ta Yi Akan PSG A Daren jiya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Cikin Girmamawa Muna Jajantawa Atiku Abubakar, Dangote, Sanata Saraki Da Dino Melaye Kan Rashin Nasarar Da Arsenal Ta Yi Akan PSG A Daren jiya Bayan su, wane Babba kuka sani dan Arsenal a kasar nan?
Gwammatin Tinubu tace zata gina makamin kare dangi, watau Nokiliya, Saidai Minista yace kul kada a fara

Gwammatin Tinubu tace zata gina makamin kare dangi, watau Nokiliya, Saidai Minista yace kul kada a fara

Duk Labarai
Ministan wutar Lantarkin Najeriya, Adebayo Adelabu ya gargadi yunkurin hukumar makamashin Najeriya na samar da tashoshin makamin Nokiliya dan samar da wutar lantarki. Hukumar dai tace tana son yin hakanne dan samar da wutar Lantarki me karfin 1,200 Megawatt da zata magance matsalat wutar Lantarkin Najeriya. Shugaban Hukumar Makamashin, Anthony Ekedewa ya kaiwa ministan wutar lantarkin ziyara a ofishinsa a Abuja ranar Talata ind ya bayyana cewa suna shirin samar da tashoshin makamin kare dangi guda 4 a Najeriya. Yace idan suka yi nasara hakan zai samar da ingantacciyar wutar Lantarki me karfi sosai a Najeriya Yace suna son kafa wadannan tashoshin wutar ne a jihohin Kogi da Akwa-Ibom. Saidai yace basu da kudi amma suna neman hada kai da ma'aikatar wutar Lantarkin. Mini...
Budurwa ta yi karyar An yi garkuwa da ita, ashe dakin saurayinta ta tafi suka buga soyayya

Budurwa ta yi karyar An yi garkuwa da ita, ashe dakin saurayinta ta tafi suka buga soyayya

Duk Labarai
Wata daliba dake ajin karshe na jam'ar Jihar Ekiti, EKSU me suna Helen Kayode ta yi karyar an yi garkuwa da ita amma ashe dakin saurayinta ta tafi suka sha soyayya. Ta aikawa kanwarta da sakon cewa, ta shiga motar da ba ta gane mata ba inda daga baya tace an kaita wani kango ana tsare da ita. Sakon nata ya watsu sosai a kafafen sada zumunta sannan hankalin mutanen Iworoko-Ekiti da Ado-Ekiti ya tashi sosai inda daga canne ta fito. Kakakin 'yansandan jihar, SP Sunday Abutu ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace sun kama dalibar. Kuma ta amsa laifin data aikata na aika sakon garkuwa da ita amma na karya. Hukumar 'yansandan sun yi gargadin cewa kada a sake samun wanda yayi hakan in ba haka ba mutum zai fuskanci hukunci
Tabbas na bayar umarnin a ciro min kàn Wike sannan a kàshè Tinubu inda har nasa  ladar Naira Miliyan 100 ga wanda yayi hakan>>Nnamdi Kanu

Tabbas na bayar umarnin a ciro min kàn Wike sannan a kàshè Tinubu inda har nasa ladar Naira Miliyan 100 ga wanda yayi hakan>>Nnamdi Kanu

Duk Labarai
Shugaban haramtacciyar kungiyar IPOB dake son lafa kasar Biafra, Nnamdi Kanu ya aminta cewa ya sa a kashe masa ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ta hanyar ciro kansa. Sannan kuma yasa a kashe shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da kona kadarorinsa, inda har ya saka ladar Naira Miliyan 100 ga duk wanda yayi hakan. Wani shaida ne ya bayyana hakan a kotu inda yace Kani ya fadi hakanne a gidan Rediyon da ya bude. An kuma saurari maganar da Kanu yayi wadda aka nada a cikin Kotun inda aka jishi ana cewa, a kashe Wike saboda bai cancanci rayiwa ba sannan a kashe Tinubu a kona kadarorinsa sannan a kashe jami'an tsaro.
‘Yan gida daya su 5 sun mùtù bayan cin Abinci me guba

‘Yan gida daya su 5 sun mùtù bayan cin Abinci me guba

Duk Labarai
Wasu 'yan gida daya su 5 sun mutu bayan cin abinci me guba a garin Ogidi, dake karamar hukumar Idemili North ta jihar Anambra. Mahaifiyar su ma na can kwance rai hannun Allah a Asibiti. Lamarin ya faru ranar Asabar 3 ga watan Mayu 2025 kuma ya jefa mutanen garin cikin damuwa. Mahaifin yaran Pa Robinson Aghalu dan shekaru 76 wanda tsohon soja ne yace yaran nasa sun fara amai da ciwon ciki ne bayan cin abincin da mahaifiyarsu ta dafa. Su 6 ne suka ci abincin kuma guda 5 sun mutu. Kakakin 'yansandan jihar, SP Tochukwu Ikenga ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace sun dauki abincin dan zuwa a yi gwaji.
Ji Dalilin da yasa Hukumar EFCC suka naɗe Gudaji Kazaure zuwa Abuja

Ji Dalilin da yasa Hukumar EFCC suka naɗe Gudaji Kazaure zuwa Abuja

Duk Labarai
Hukumar EFCC a jihar Kano ta kama tsohon ɗan majalisar tarayya Hon. Muhammad Gudaji Kazaure bayan ta gayyaceshi ofishinta kuma ya kai kansa amma daga bisani ta naɗeshi zuwa Abuja. Bayanan da Zuma Times Hausa ta samu sun ce, EFCCin tana neman bayanan wasu kyaututtukan kudade naira miliyan 14 da suka shiga asusun bankin tsohon dan majalisar a wani lokaci a shekarar 2019. Me zaku ce?
Dalibar Da Ta Kammala Digiri Da Sakamako Mafi Daraja A Jami’ar Northwest Dake Kano Ta Koma Tallar Wainar Fulawa Bayan Rashin Samun Aikin Yi

Dalibar Da Ta Kammala Digiri Da Sakamako Mafi Daraja A Jami’ar Northwest Dake Kano Ta Koma Tallar Wainar Fulawa Bayan Rashin Samun Aikin Yi

Duk Labarai
Dalibar Da Ta Kammala Digiri Da Sakamako Mafi Daraja A Jami'ar Northwest Dake Kano Ta Koma Tallar Wainar Fulawa Bayan Rashin Samun Aikin Yi. A yayin jin ta bakin Kwamared Habiba Usman Garkuwa, wadda har ta taba zama shugabar dalibai na jami'ar da ta yi, ta ce ta raba takardun neman aiki adadin da ba za ta iya tunawa ba, amma har yanzu shiru don haka ta yanke shawarar fara soya wainar fulawa da awara. Habiba dai ta fita da sakamako mafi daraja Jami'ar Northwest a shekarar 2024 a fannin ilimin kimiyyar Biology, kamar yadda wanda ya fitar da rahoton, Abdulwahab Said Ahmad ya wallafa a Shafinsa na Facebook.
An kama Barawo bayan da ya saci Keke Napep a masallaci a jihar Naija

An kama Barawo bayan da ya saci Keke Napep a masallaci a jihar Naija

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan jihar Naija sun yi nasarar kama wani barawon Keke Napep a jihar. Kakakin 'yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace lamarin ya farune ranar 5 ga watan April. Sunan Barawon da aka kama Abdulaziz Salisu kuma yayi satar ne yayin sallar Asuba a Dakwa. Yace bayan ya saci Keke Napep din yayi yunkirin kaiwa wani me suna Abubakar Mohammed dan ya sayar masa dashi. Yace ana tsaka da sallah ne Abdulaziz ya fita ya sace Keke Napep din amma sai 'yansanda suka kamashi a gadar Maje inda ya amsa cewa satota yayi.