Tuesday, December 23
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Hukumar Kula da jami’o’in Najeriya, NUC tace wadanda aka baiwa Digirin Girmamawa irin wadda aka baiwa Rarara su daina Amfani da sunan “Dr.” A jikin sunansu

Hukumar Kula da jami’o’in Najeriya, NUC tace wadanda aka baiwa Digirin Girmamawa irin wadda aka baiwa Rarara su daina Amfani da sunan “Dr.” A jikin sunansu

Duk Labarai
Hukumar kula da jami'o'in Najeriya NUC ta gargadi masu Digirin girmamawa ta Doctorate da cewa su daina amfani da "Dr." A gaban sunansu. Hukumar tace wadanda suka yi karatun PhD ne kadai ke da ikon amfani da "Dr." A gaban sunansu. Shugaban hukumar ta NUC, Prof. Abdullahi Ribadu ne ya bayyana haka a wajan kaddamar da wani bincike da aka gudanar akan bayar da Digirin Doctorate na girmamawa da jami'o'i ke yi. Ya bayyana cewa akwai damuwa kan yanda ake amfani da Digirin Doctorate na girmamawa ta hanyar da bata kamata ba
Da Nine Shugaban kasa da Tuni na goyi bayan Trump ya kawo Khari Najeriya>>Inji Peter Obi

Da Nine Shugaban kasa da Tuni na goyi bayan Trump ya kawo Khari Najeriya>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa a shekarar 2023 a jam'iyyar Labour Party, Peter Obi ya bayyana cewa, da shine shugaban kasa a yanzu da tuni ya baiwa shugaban kasar Amurka, Donald Trump damar kawo Khari Najeriya. Ya bayyana hakane a wajan wani taro da aka yi dakan shugabanci. https://www.youtube.com/watch?v=8hsf2Ufy31c Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana aniyar kawo Khari Najeriya dan kawar da wadanda ya kira 'yan ta'adda masu yiwa Kiristoci Khisan Kyiyashi. Lamarin ya jawo takaddama inda gwamnatin Najeriya tace ba gaskiya bane ba'a yiwa Kiristoci Khisan Kyiyashi a Najeriya.
Kalli Bidiyon inda wasu ke cewa ashe Raba Gardama Dan Iyskane? Bayan da aka ga ya mikawa Abokiyar aikinsa, Maryam Shu’aib hannu su gaisa amma taki yadda

Kalli Bidiyon inda wasu ke cewa ashe Raba Gardama Dan Iyskane? Bayan da aka ga ya mikawa Abokiyar aikinsa, Maryam Shu’aib hannu su gaisa amma taki yadda

Duk Labarai
Wani Bidiyo Tauraron fina-finan Hausa, Raba Gardama ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta. An ganshi a wajan tarone tare da abokan aikisa, Amal Umar da kuma Maryam Shuaib. Ya mikawa Maryam hannu dan su gaisa amma sai ta dukar da kanta kasa, ta ki yadda. Wasu sun rika cewa, Ashe Raba Gardama Dan iskane da dai magangani masu kama da hakan. Inda wasu kuma suka ce Maryam ta ki bashi hannune saboda a idon Duniyane. https://www.tiktok.com/@turakees.shot/video/7575680532667796757?_t=ZS-91dPZQalphI&_r=1
Allah Sarki: Kalli Bidiyon matar Gfresh, Maryam inda ta tabbatar da cewa ya sake ta, tace ta yi hakuri iya bakin kokarinka dan ta zauna dashi amma ya Wùlàkànta Aure, ya je ya tare da Tsohuwar matarsa, Sadiya Haruna

Allah Sarki: Kalli Bidiyon matar Gfresh, Maryam inda ta tabbatar da cewa ya sake ta, tace ta yi hakuri iya bakin kokarinka dan ta zauna dashi amma ya Wùlàkànta Aure, ya je ya tare da Tsohuwar matarsa, Sadiya Haruna

Duk Labarai
Matar tauraron Tiktok G-fresh Al-Amin Maryam ta tabbatar da cewa mijin nata ya sake ta saki daya. Tace ya aika mata da sakon Sakin. Tace ya koma ya tare da tsohuwar matarsa, Sadiya Haruna. Danna nan da kallin Bidiyon https://www.tiktok.com/@xainabibraheem/photo/7575680629979860245?_r=1&_t=ZS-91dIjIeIJeb Amma tace zai dawo ya nemeta sanda kuma ba zai ganta ba. A wani Bidiyo kuma da aka ganta ana mata kyautar wayar iPhone 14 tace ta yi iya kokarinta wajan ganin ta zauna da Gfresh ta yi hakuri amma ya wulakanta Aure, tace dik wanda ya wulakanta aure, Aure sai ya wulakanta shi. Tace ita kuma tasan hakurin da ta yi ba zai tafi a banza ba. https://www.tiktok.com/@maryamnikicminaj/video/7575568420083617045?_t=ZS-91dGn6rbgmW&_r=1 Kalli Bidiyon anan Haka...
Hukumar ‘yansandan Najeriya ta fitar da Jadawalin makarantun da tshàgyèràn Dhàjì ke shirin shiga a Arewa

Hukumar ‘yansandan Najeriya ta fitar da Jadawalin makarantun da tshàgyèràn Dhàjì ke shirin shiga a Arewa

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan Najeriya ta fitar da bayanan gargadi inda take cewa, 'yan Bindiga na ta kwarara zuwa jihar Kogi. Tace hakan na faruwane saboda su gujewa luguden wuta da ake musu a jihohin Naija da Kwara. Hakanan sanarwar wadda kafar Sahara reporters ta ce ta samo ta bayyana cewa, tshageran Dhajin na shirin kai hari kan makarantun Ochaja Boys and Girls Secondary Schools da kuma jami'ar Prince Abubakar Audu University, Anyigba, da bankuna da guraren Ibada da ofisoshin 'yansanda. Sanarwar tace tshageran Dhajin na dauke da muggan makamai masu hadarin gaske.
Kalli Bidiyon tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yana fadin cewa Gwamnatin Tarayya tana Baiwa tshàgyèràn Dhàjì kudi da kayan Abinci, inda yayi zargin cewa Jihar Kaduna Biliyan 1 ta basu

Kalli Bidiyon tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yana fadin cewa Gwamnatin Tarayya tana Baiwa tshàgyèràn Dhàjì kudi da kayan Abinci, inda yayi zargin cewa Jihar Kaduna Biliyan 1 ta basu

Duk Labarai
Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi zargin cewa hanyar da Gwamnatin yanzu ta dauka itace ta baiwa tsageran Daji kudi da kayan abinci wai dan a rika lallabasu kada su rika kai hare-hare kan al-umma. Yace jihohi da yawa na Arewa na kan wannan tsarin ciki hadda jihar Kaduna. Malam ya kara da cewa a jihar Kaduna Naira Biliyan 1 aka baiwa tsageran dajin. Yace suna da hujjoji akan hakan kuma idan lokaci yayi zasu fitar dasu. Malam ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV. https://twitter.com/OurFavOnlineDoc/status/1992320400940990504?t=XMHE9ZcFNCFV6pbOc6vpfA&s=19
Sàtàr Dàlybàì: Kalli Bidiyon Yanda Tshàgyèràn Dhàjì suke cewa an sa inda suke a zo a kubutar da Dàlybàn idan a isa

Sàtàr Dàlybàì: Kalli Bidiyon Yanda Tshàgyèràn Dhàjì suke cewa an sa inda suke a zo a kubutar da Dàlybàn idan a isa

Duk Labarai
Wani Bidiyo ya bayyana a kafafen sada zumunta dake nuna wani da aka bayyana a matsayin daya daga cikin 'yan Bindigar da suka sace daliban makaranta. A cikin Bidiyon an jishi yana cewa, ai an san inda suke a zo a kubutar da daliban idan an isa. Lamarin ya dagawa mutane hankula inda da yawa ke cewa lallai akwai matsala idan har dan Bindiga zai iya fitowa yana wannan kalami. https://twitter.com/vdmempire/status/1992317756092367307?t=EXfZKPEV8SB3ovG3HKX9JA&s=19
Kalli Bidiyon: Wannan Bafulatanin Makiyayi ya dauki Hankula bayan da yace sun Làlàtà gonar Fasto data malam Hisabi sai a Lahira

Kalli Bidiyon: Wannan Bafulatanin Makiyayi ya dauki Hankula bayan da yace sun Làlàtà gonar Fasto data malam Hisabi sai a Lahira

Duk Labarai
Wannan wani Bafulatanine da ya bayyana cewa sun lalata gonar Fasto data malam Hisabi sai a Lahira. Bidiyon nasa ya dauki hankula a kafafen sada zumunta wanda hakan ke kara tabbatar da cewa kowane bangare na shan wahala a hannun Fulanin. https://twitter.com/MFaarees_/status/1991771368057368813?t=8VrKpVEzRO58Z5OdF4UPvg&s=19