Falalar Goma na karshe daga bakin Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa
Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na Najeriya kuma shugaban hukumar Hizba ta jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ce duk da cewa dukkannin ranaku da dararen watan Ramadan na da falala amma kwanaki 10 na ƙarshen watan sun fita daban.
"Goman ƙarshe na da wasu abubuwa guda uku masu muhimmancin kuma wannan ne ma ya sa ake fifita goman ƙarshen a kan goman farko da na tsakiya." In ji Sheikh Daurawa.
Allah ya yi rantsuwa da darare 10: Na farko dai Allah ya yi rantsuwa da su inda a cikin Alƙur'ani ya ce Wal Fajr, Wa Layalil A'shar. Malamai sun ce wannan na nuni da kwanakin ƙarshe na Ramadan ko kuma goman farko na watan Zulhijja.
Daren Laylatul Qadr ya faɗo a goman ƙarshe: Abu na biyu a cikin wannan watan akwai daren Laylatul Qadr. Idan mutum ya yi dace a daren 21 ko 23 ko ...








