Saturday, February 14
Shadow

Author: Bashir Ahmed

ILMI KOGI: Za Mu Iya Sàìťawa Mutum Kaddara Mai Kyau Tare Ďa Ķýawàwàɲ Dabi’u Tun Kafin Samun Cikinsa Zuwa Ya Zo Duniya, Inji Imam Assufiyyu

ILMI KOGI: Za Mu Iya Sàìťawa Mutum Kaddara Mai Kyau Tare Ďa Ķýawàwàɲ Dabi’u Tun Kafin Samun Cikinsa Zuwa Ya Zo Duniya, Inji Imam Assufiyyu

Duk Labarai
Imam Habibi Abdallah Assufiyyu, shahararren Malami kuma Shugaban Kungiyar Malamai Masana Ilimin Taurari Na Kasa (FANIS) ya ce "Muna iya śàìțàwa wanda ba a haifa ba kýaķķýawan kaddara da dabi'u masu inganci tun kafin a samu cikin sa zuwa a haife shi ya zo duniya, a karshe kuma ya samu muwafaka mai girma a rayuwa. Saboda haka wannan al'amari ne da iyaye ya kamata su maida hankali akai domin samarwa 'ya'yan su kyakkyawar gobe. Shehin Malamin ya kara da cewa "Kuma a shirye muke domin taimaka ma dukkan wanda yake son ya ga haka ta faru ga rayuwar 'ya'yansa, wanda zai sa su samu sauki wajen tarbiyar 'yantar da su a rayuwa". Ta hanyar amfani da Ilimin Falaki dan Adam zai samu ingantacciyar rayuwa mai cike da tsari da manyan nasarori wadanda tunani ko hankali bazai iya hikayo su ba, batare d...
Shugaba Tinubu Ya Tallafawa Ma’aikata Da Ɗalibai Da Gudummawar Motocin Sufuri

Shugaba Tinubu Ya Tallafawa Ma’aikata Da Ɗalibai Da Gudummawar Motocin Sufuri

Duk Labarai
Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu ya cika alƙawarin da yayi na ba da kyautar motoci ga ƙungiyoyin ƙwadago da na ɗalibai domin sauƙaƙa musu harkokin sufuri. An ƙaddamar da ba da motocin yau a fadar shugaba ƙasa, Abuja inda aka miƙa motocin bas-bas guda (64) masu amfani da iskar gas ta (CNG) ga shugabancin ƙungiyoyin. Idan ba a manta ba, tun bayan cire tallafin man fetur ne dai shugaban ƙasar yayi alƙawarin tallafa wa ma'aikata da ɗalibai da motocin sufuri masu amfani da iskar Gas waɗanda za su rage musu kashe kuɗaɗe wajen zirga-zirgarsu ta yau da kullum.

Maganin yawan tusa

Kiwon Lafiya, Magunguna
Cin abincin dake da wahalar narkewa ko shan wasu kalar magunguna na sa a rika yin tusa da yawa. Yawanci dai Tusa na da alaka da kalar abincin da mutum ke ci ne ko kuma wata rashin lafiya. Wata tusar na da kara, wata bata da kara yayin da wata ke da wari wata kuma bata da wari, ko ma dai menene masana kiwon lafiya sun ce mafi yawan mutane sukan yi tusa sau 10 zuwa 20 a rana. Mafi yawan abincin dake kawo Tusa sun hada da Wake ko ganye wanda ba'a dafa ba, irin su latas, da shan madara, lemun kwalba, Alkama da sauransu. Sauran abubuwan dake kawo yawan tusa sun hada da shan Alewa,shan taba, shan giya,shiga yanayi na matsi ko damuwa, Yin tusa ba matsala bane amma idan ta yawaita tana iya zama illa ga mai yinta. Ana iya samun waraka daga yawan tusa ta hanyar canja kalar abincin da...
JARABTA: Cikin Kwanaki Uku A Jere, Ya Rasa Matarsa Da Yaransa Biyu

JARABTA: Cikin Kwanaki Uku A Jere, Ya Rasa Matarsa Da Yaransa Biyu

Duk Labarai
JARABTA: Cikin Kwanaki Uku A Jere, Ya Rasa Matarsa Da Yaransa Biyu. Wannan bawan Allah mai suna Adamu Manzo ya gamu da jarabawar rashi. Shekaran jiya Lahadi babban d’ansa ya rasu aka yi masa jana’iza jiya Litinin, bayan an dawo daga makabarta jaririn da aka haifa masa da kwana d’aya ya rasu shi ma aka yi jana’izar sa, inda a jiya Litinin din, Allah mai yin yadda Ya so sai kuma ga shi an wayi gari da rasuwar matar sa wacce ita ce mahaifiyar yaran guda biyun da suka rasu. Tuni aka yi mata sallar jana’iza a safiyar yau Talata a unguwar Dawaki Kofar Sarkin Doya, dake jihar Gombe. Hakika wannan jarrabawa ta girmama matuka. Allah Ya gafarta musu.
Kuma Dai: Kalli Bidiyon tsiraicin hafsat baby na 3 ya fita shima anata Allah wadai

Kuma Dai: Kalli Bidiyon tsiraicin hafsat baby na 3 ya fita shima anata Allah wadai

Jaruman Tiktok, Nishadi
A yayin da ake ci gaba da mamakin Bidiyon Hafsat Lawancy tsirara wanda ke ta yawo a shafukan sada zumunta, karin Bidiyo yinta wanda take tsirara-tsirara na kara bayyana. A jiya dai an ga Karin wani Bidiyo da take irin rawar da ta yi a Bidiyon tsiraicin amma a wannan karin tana sanye da riga wadda ta rufe tsiraicinta kadan. Hakanan a yau ma wani sabon bidiyon Hafsat dinne ya sake bayyana inda aka ganta sanye da wata riga irin ta turawa tana dai juya mazaunanta. Tuni dai hukumar Hisbah dake Kano ta kama Hafsat. Kalli Bidiyon anan
Wata Sabuwa An gano cewa Hafsat Lawancy ba ta san namiji ba virgin ce

Wata Sabuwa An gano cewa Hafsat Lawancy ba ta san namiji ba virgin ce

Duk Labarai
Wata kungiya dake ikirarin ta matane masu tsafta wanda basu san Namiji ba wanda ake kira da Virgin a turance tace ta binciki Hafsat Baby ko Hafsat Lawancy wadda Bidiyonta tsirara ya bayyana. Kungiyar tace ta gano Hafsat bata san Namiji ba, Virgin ce. https://twitter.com/softsopheee/status/1838272662197395732?t=PONLSkozEMD_3yxROuZ3wA&s=19 Kungiyar ta kuma ce tuni ta baiwa Hafsat shahada dake nuna cewa ita virgin ce bata san Namiji ba.
Bidiyon tsiraicin hafsat baby: Ji Abinda Sheikh Aminu Daurawa yayi da Bidiyon

Bidiyon tsiraicin hafsat baby: Ji Abinda Sheikh Aminu Daurawa yayi da Bidiyon

Duk Labarai
A safiyar Litinin ce Sheikh Daurawa ya wallafa bidiyon Hafsat Baby tare da wasu mata da hukumar ta kama. Wasu majiyoyi a Hukumar Hisbah ta Jihar Kano sun tabbatar wa Aminiya cewa Hafsan Baby tana tsare a hannun hukumar. Sai dai sun ƙi su bayyana lokacin da hukumar ta cika hannu da jarumar TikTok ɗin. Aminiya ta lura cewa bayan kimanin sa’o’i biyu, Sheikh Daurawa wanda a halin yanzu yake ƙasar Jamus, ya goge sakon bidyon kamen Hafsat. Ana iya tuna cewa a kwanakin baya hukumar ta sanar cewa an yi kutse a shafinta, lamarin da ya sa a halin yanzu ba za iya dogaro da wani daga shafin ba. Aminiya ta yi ƙoƙarin zantawa da jami’an Hisbah kan kamen Hafsat Baby, amma hakan bai samu ba. Jami’an da muka tuntuɓa sun bayyana cewa kasancewar Litinin ɗin ranar hutun Takutaha ce da Gwamna...
Ina baiwa gwamnati Shawarar ta cire tallafin man fetur gaba daya>>Dangote

Ina baiwa gwamnati Shawarar ta cire tallafin man fetur gaba daya>>Dangote

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa,yana baiwa gwamnatin tarayya shawarar cire tallafin man fetur gaba daya. Dangote ya koka da cewa farashin gas a Najeriya na da sauki matuka wanda na kasar Saudiyya ma yafi na Najeriya tsada. Yace kasashe ciki hadda saudiyyar duk sun cire tallafin man fetur din amma an bar Najeriya a baya. Dangote ya bayyana hakane a wata hira da kafar Bloomberg ta wallafa. Yace kuma cire tallafin man da baiwa matatarsa dama zai sa a san ainahin yawan man fetur din da 'yan Najeriya ke sha wanda a yanzu ba'a sani ba.