Thursday, April 16
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Jihar Gombe ta kulla yarjejeniya da kamfanin kasar China dan samarwa da kanta wutar Lantarki

Jihar Gombe ta kulla yarjejeniya da kamfanin kasar China dan samarwa da kanta wutar Lantarki

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Gombe ta samarwa da kanta hanyar samun wutar lantarki wadda ba sai ta dogara da gwamnatin tarayya ba. Gwamnatin ta sakawa wata yarjejeniyar samar da wutar me karfin megawatt 100 daga hasken Rana hannu tare da kamfanin China18th Engineering na kasar China. Gwamnan jihar Inuwa Yahya ya bayyana cewa, hakan zai basu damar karfafa huldar kasuwanci a jihar. Yace kudirin dokar da majalisa ta yi da ya baiwa jihohi damar samarwa da kansu wutar lantarki da rabata ne ya basu damar kaiwa ga wannan mataki.
Kalli yanda wani bature ya ke zaune a Kauyen Legas inda yace abinda ke burgeshi shine baya biyan kudin haya

Kalli yanda wani bature ya ke zaune a Kauyen Legas inda yace abinda ke burgeshi shine baya biyan kudin haya

Duk Labarai
Wani bature dake zaune a Kauyen Legas ya bayyana cewa, Abinda ke burgeshi shine baya biyan kudin haya. Bauturen na zaunene a kauyen Legas da ake kira Makoko wanda ke akan ruwa. https://twitter.com/whatsappblog9ja/status/1853830143988343061?t=1fO--driHjmkmz2HNDONxQ&s=19 Kuma an shiga dashi ya nuna ko ina a cikin dakinsa. An tambayeshi me yasa be je unguwar masu kudi ya zauna ba, sai ya kayar da baki yace idan dai ka iya zama da mutane lafiya, babu inda ba zaka je ka zauna ba.
Lalacewar wutar Lantarki:Majalisa ta gayyaci ministoci dan binciken yanda aka yi da Dala Biliyan $2 da aka bayar da samar da wutar Lantarki

Lalacewar wutar Lantarki:Majalisa ta gayyaci ministoci dan binciken yanda aka yi da Dala Biliyan $2 da aka bayar da samar da wutar Lantarki

Duk Labarai
Majalisar wakilai ta gayyaci ministoci 3 da suka hada da na Noma, da samar da abinci, Abubakar Kyari da na kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire, Uche Nnaji, dana kasafin kudi da tsare-tsare, Atiku Bagudu dan su mata bayani kan yanda aka kashe Dala Biliyan $2 da aka bayar dan samarwa da Najeriya wutar lantarki. Kwamitin kula da makamashi na zamani na majalisar ne suka gayyaci ministocin. Kudin an samo su ne daga tallafi da kuma zuba jari dan samarwa da Najeriya wata hanya ta daban ta samun wutar lantarki banda wadda ake da ita. Kuma an samu kudinne daga shekarar 2015 zuwa yanzu. A ranar Talata da Larabane dai ministocin zasu gurfanar gaban majalisar dan bayar da ba'asi kan yanda aka kashe wadannan kudade. Majalisar ta nuna damuwa kan cewa duk da wadannan kudade amma gashi wut...
Muna da Hujjojin cewa kun aikata laifin cin amanar kasa amma dai Tausayine yasa muka yafe muku>>Gwamnatin Tarayya ta gayawa kananan yaran da ta yiwa Afuwa

Muna da Hujjojin cewa kun aikata laifin cin amanar kasa amma dai Tausayine yasa muka yafe muku>>Gwamnatin Tarayya ta gayawa kananan yaran da ta yiwa Afuwa

Duk Labarai
Kananan yaran da aka kama aka gurfabar a kotu bisa zargin cin amanar kasa da yunkurin kifar da gwamnatin shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu amma Shugaban ya yafe musu sun koma gida Kano. Kamin komawarsu, sai da suka je fadar shugaban kasa suka gana da mataimakin shugaban kasar, Kashim Shettima inda ya bayyana musu cewa suna da Bidiyo da hotuna dake nuna cewa sun aikata laifi amma tausayi irin na shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ne yasa ya yafe musu. Ya bayyana cewa zanga-zangar tsadat rayuwa ta jawo asarar Naira Biliyan 300. Ya jawo hankalin matasan da cewa kada su yadda ayi amfani dasu wajan tayar da fitina inda yace wannan dama ce da suka sake samu ta su zama na gari. Tuni dai aka mika su hannun gwamnan jihar ta Kano Abba Kabir Yusuf ina shima ya daukesu zuwa gida.
Najeriya ta fada Duhu yayin da matsalar wutar lantarki ta sake aukuwa, Ji Jihohinnda lamarin ya shafa

Najeriya ta fada Duhu yayin da matsalar wutar lantarki ta sake aukuwa, Ji Jihohinnda lamarin ya shafa

Duk Labarai
'Yan Najeriya sun fada duhu biyo bayan sake samun matsala da wutar lantarkin kasar ta yi. Wannan shine karo na 3 da wutar lantarkin kasar ke samun matsala a shekarar 2024. Da Misalin karfe 1:50 pm. Na ranar Talata ne wutar lantarkin ta sake samun matsala. Kamfanin kula da wutar na kasa,TCN ya tabbatar da hakan amma yace ba gaba daya wutar bace ta samu matsala. Kakakin hukumar, Ndidi Mbah ne ya tabbatar da hakan inda yace injiniyoyinsu na aiki tukuru dan dawo da wutar. Ya kara da cewa An samu dawo da wutar a babban birnin tarayya Abuja kuma suna kokarin dawo da ita a sauran jihohi.
Bayan da ya tsere daga Najeriya, Dan Daudu Bobrisky ya wallafa Bidiyo yana kirga daloli

Bayan da ya tsere daga Najeriya, Dan Daudu Bobrisky ya wallafa Bidiyo yana kirga daloli

Duk Labarai
Shahararren dan daundu, Bobrisky wanda ya sha dambarwar kame daga hukumomin Najeriya amma daga baya ya samu tsallakewa zuwa kasar waje ya sake bayyana. Ya wallafa hotunan Bidiyo yana wasa da dalolin Amirka. https://twitter.com/Chrisvlognation/status/1853869625794302249?t=oy2yERZfQhy_nqkrTmyhlw&s=19 Wani har ya tsokaneshi da cewa aro kudin yayi amma ya mayar masa da martanin cewa a Najeriya ne ake iya yin haka amma banda kasar waje. Bobrisky ya kara da cewa, Wani masoyinsa ne ya bashi wadannan kudade.
Jami’in Hukumar NSCDC ya yanke jiki ya fadi ya mutu jim kadan bayan da aka masa karin girma

Jami’in Hukumar NSCDC ya yanke jiki ya fadi ya mutu jim kadan bayan da aka masa karin girma

Duk Labarai
Jami'in hukumar tsaro ta NSCDC Opatola wanda ba'a dade da karawa mukami ba ya yanke jiki ya fadi ya mutu jim kadan bayan an biyashi Albashi. Yana aiki ne a Iwo kuma ya mutu ne bayan da ya shiga ban daki kamar zai biya bukatarsa. Wasu shaidu sun bayyanawa jaridar The Nation cewa mutumin ya je wajan aiki lafiya kalau a ranar da ya mutu. Abokan aikinsa sun ce sun ga Albashinsu suna korafi akai jim kadan kawai aka ce ai ya mutu.