Sunday, January 18
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Bidiyo: Wannan Mutumin yace wai an masa Wahayin ya kera jirgin ruwa saboda ranar Kirsimeti Duniya zata tashi

Bidiyo: Wannan Mutumin yace wai an masa Wahayin ya kera jirgin ruwa saboda ranar Kirsimeti Duniya zata tashi

Duk Labarai
Wani mutum dan kasar Ghana yace wai an masa wahayi cewa nan da ranar Kirsimeti, 25 ga watan Disamba, Duniya zata tashi. Yace wai an Umarceshi da ya kera jirgin ruwa irin na Annabi Nuhu(AS). Yace yan kan kera Jiragen guda 8 manyamanya wadanda kowanensu zasu dauki mutane akalla Miliyan 600. Ya nemi duk wanda suka yadda dashi su zo su tayashi aiki. A cewarsa wai za'a yi ruwa irin na Dufana. https://www.tiktok.com/@ebonoah/video/7554531904482069771?_t=ZS-924jLzUhgZt&_r=1
Da Duminsa: Hukumar Sojojin Saman Najeriya ta fitar da sanarwa kan jirgin saman C-130 dake Burkina Faso da sojoji 11

Da Duminsa: Hukumar Sojojin Saman Najeriya ta fitar da sanarwa kan jirgin saman C-130 dake Burkina Faso da sojoji 11

Duk Labarai
Hukumar sojojin saman Najeriya ta fitar da sanarwa game da jirgin saman C-130 da sojoji 11 dake kasar Burkina Faso. Me magana da yawun hukumar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ne ya fitar da sanarwar inda yace jirgin na kan hanya ne ya samu rangarda inda yayi saukar gaggawa a kasar ta Burkina Faso. Yace wannan shine abinda dokar kasa da kasa ta tanada. Yace jirgin bai taka kowace doka ba kuma suna nan kan bakansu na yiwa dokokin kasa da kasa biyayya. Yace sojojin Najeriyar sun samu tarba me kyau a hannun hukumomin kasar Burkina Faso kuma da zaran komai ya daidaita, zasu ci gaba da tafiyarsu.
Sabbin Rahotanni sun ce Jirgin Najeriya C-130 dake kasar Burkina Faso ya samu Tangarda ne ya sauka a kasar

Sabbin Rahotanni sun ce Jirgin Najeriya C-130 dake kasar Burkina Faso ya samu Tangarda ne ya sauka a kasar

Duk Labarai
Wasu Rahotanni daga bangaren masu goyon bayan Najeriya sun bayyana cewa jirgin saman C-130 da ke kasar Burkina Faso ba tursasa masa aka yi ya sauka ba. Jirgin ya sauka ne saboda samun Tangarda a yayin da yake kan hanya. Saidai hakan na zuwane bayan da ita kasar Burkina Faso tace jirgin ya shigar mata kasa ne ba bisa ka'ida ba. Zuwa yanzu dau hukumar sojojin saman Najeriya basu fitar da sanarwa ba game da lamarin.
Da Duminsa: Kasar Jamhuriyar Nijar tace daga yanzu duk wasu kaya da za’a shigar musu dasu daga Najeriya sai an musu daidai a ga komenene a iyaka kamin a barsu su wuce

Da Duminsa: Kasar Jamhuriyar Nijar tace daga yanzu duk wasu kaya da za’a shigar musu dasu daga Najeriya sai an musu daidai a ga komenene a iyaka kamin a barsu su wuce

Duk Labarai
Kasar Nijar ta fitar da sabuwar doka wadda tace daga yanzu duk wani abu da za'a shigar mata dashi dana Najeriya sai an masa daidai an ga komenene a ciki kamin a barshi ya wuce. Nijar din ta fitar da wannan sabuwar sanarwar ne bayan da Najeriya ta dakile yunkurin juyin mulkin a kasar Benin Republic. Hakanan sanarwar na zuwane bayan da kasar Burkina Faso ta rike jirgin saman Najeriya da sojoji 11 da suka shigar mata sararin samaniyar ta ba bisa ka'ida ba.
Duk da Allah wadan da aka yi akan Bidiyon farko, Tauraron fina-finan Hausa, Shalele ya sake yin Bidiyo Manne da Abokiyarsa

Duk da Allah wadan da aka yi akan Bidiyon farko, Tauraron fina-finan Hausa, Shalele ya sake yin Bidiyo Manne da Abokiyarsa

Duk Labarai
A jiya ne dai Bidiyon Tauraron fina-finan Hausa, Shalele ya dauki hankula bayan da aka ganshi manne jikin wata yarinya. Ba 'yan kallo kadai ba, hadda wasu daga cikin abokan kasuwancinsa sun yi Allah wadai da wannan Bidiyon. Saidai a yau ma an sake tashi da wani Bidiyonsa tare da da Budurwar da suka yi Bidiyon farko. https://www.tiktok.com/@yardaraja0/video/7581618452272663826?_t=ZS-924cfDDga1Z&_r=1
Da Duminsa: EFCC sun sake kama Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami

Da Duminsa: EFCC sun sake kama Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami

Duk Labarai
Rahotanni daga Abuja na cewa hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC sun sake kama tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami. Sahara Reporters sun ruwaito cewa EFCC sun kama Abubakar Malami ne da yammacin jiya, Latinin. Sannan yanzu haka yana ta kokarin ganin ya samu manyan sakatarorin gwamnati 2 ne da zasu tsaya masa a bayar da belinsa. Ana zargin Malami ne da aikata ba daidai ba da kudaden da aka kwato na tsohon shugaban kasa, Marigayi janar Sani Abacha. Zargin da Malami ya dade da karyatawa.
Kalli Bidiyon: Brekete Family ta wallafa Hoton Malam Nura wanda ake zargi da yiwa yara 9 Lìywàdhì a Abuja

Kalli Bidiyon: Brekete Family ta wallafa Hoton Malam Nura wanda ake zargi da yiwa yara 9 Lìywàdhì a Abuja

Duk Labarai
Kafar Brekete Family ta wallafa Hoton Malam Nura da ake zargi da yiwa yara 9 lùwàdì a Abuja. Sannan an kira mahaifinsa inda yace an kara gishiri a labarin da matan ke bayarwa. Mahaifin nasa yace da aka fara zargin dansa, da kansa ya daukoshi ya mikawa hukuma amma gashi yanzu ana masa karyar wai shi ya koyawa da nasa yin Luwadin. Sannan ba kamar yanda aka watsa a baya ba, cewa, 'yansanda sun saki Nura, Ordinary President ya ce sun samu rahoton cewa Nura na gidan yari. https://www.tiktok.com/@minuwa365/video/7581583938397719815?_t=ZS-924X1Aqw1T7&_r=1 https://www.tiktok.com/@minuwa365/video/7581736713567915271?_t=ZS-924Xt54qRl2&_r=1
Kalli Bidiyon: Bayan “wulakancin” Matar Shugaban kasa, Remi Tinubu tawa Gwamnan Jihar Osun, An kuma ga abinda tawa matar tsohon shugaban kasa, Patience Jonathan wanda wasu ke cewa yama fi abinda tawa Gwamnan Osun Muni

Kalli Bidiyon: Bayan “wulakancin” Matar Shugaban kasa, Remi Tinubu tawa Gwamnan Jihar Osun, An kuma ga abinda tawa matar tsohon shugaban kasa, Patience Jonathan wanda wasu ke cewa yama fi abinda tawa Gwamnan Osun Muni

Duk Labarai
A jiyane aka ga yanda matar shugaban kasa, Remi Tinubu ta cewa gwamnan jihar Osun ta bashi minti 5 ya kammala jawabin da yake inda tace ya kauce ya basu guri ya ishesu da wakoki. Saidai a wajan taron dai, an kuma ji abinda matar shugaban kasar ta cewa matar tsohon shugaban kasa, Dame Patience Jonathan. Matar shugaban kasar ta kira Patience Jonathan da Mama p, Kin yi murmushi kuwa? Wasu dai sunce wannan magana bata dace ba inda wasu ke ganin hakan ba wani abu bane. https://twitter.com/warrisentinel/status/1997985889624932777?t=tlkvFjjdiXNQ6evFdNW-Sw&s=19
Bidiyon yanda wasu ke hada manja a kudu ta hanyar kara masa kala dan yayi jaa sosai ya jawo cece-kuce sosai a kafafen sadarwa

Bidiyon yanda wasu ke hada manja a kudu ta hanyar kara masa kala dan yayi jaa sosai ya jawo cece-kuce sosai a kafafen sadarwa

Duk Labarai
Wani Bidiyo da ya nuna yanda wasu ke hada manja ta hanyar kara masa kala dan yayi jaa sosai a kudancin Najeriya ya jawo cece-kuce sosai. Bidiyon ya dagawa mutane hankali sosai inda aka rika kiran gwamnati ta dauki mataki kan lamarin. An yi kira ga hukumar NAFDAC da su tsaurara bincike kan lamarin dan daukar matakan da suka dace. https://twitter.com/MobilePunch/status/1998005924200325415?t=hoDbM7E6PQ3WTPmxAzeUFQ&s=19