Sunday, April 26
Shadow

Duk Labarai

Shugaba Tinubu na sha zazzafar suka saboda wani abu da yayi da ya jawowa Najeriya abin magana

Shugaba Tinubu na sha zazzafar suka saboda wani abu da yayi da ya jawowa Najeriya abin magana

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na shan suka saboda wallafa hoton da ake zargin an yishi da AI(watau hoton Boge) Shugaban ya wallafa hotonne ta shafinsa na X. Ya wallafa cewa yana tare da shugaban kasar Rwanda, Paul Kagame inda aka gansu tare zaune. Saidai an gano cewa hoton da AI aka yishi. Hakan ya jawowa shugaban kasar suka sosai inda da yawa suka ce hakan abin kunyane ga Najeriya. https://twitter.com/i/status/2007850631579529506 https://twitter.com/i/status/2007941035385909582 https://twitter.com/i/status/2008038389296021750
Kalli Bidiyon: Kai Duniya, Wannan ‘yan Matan sun dauki hankula bayan da Mahaifinsu ya rasu suka ce ba zasu je kan gawarsa ba

Kalli Bidiyon: Kai Duniya, Wannan ‘yan Matan sun dauki hankula bayan da Mahaifinsu ya rasu suka ce ba zasu je kan gawarsa ba

Duk Labarai
Wadannan matasan 'yan matan sun dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da mahaifinsu ya rasu amma suka ce ba zasu hakarci jana'izar su ba. Sun bayyana cewa, tun suna kananan yara ya barsu, bai san cinsu ba, bai san shan su ba, sannan a yanzu idan aka zo neman aurensu cewa ake shegune. Sun bayyana cewa, ko Sallah suka yi ba zasu masa addu'a ba. https://www.tiktok.com/@fatima.yakubu54/video/7591445440088837397?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7591445440088837397&source=h5_m&timestamp=1767546204&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_ca...
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Daya daga cikin manyan malaman Arewa ya bayyana cewa kasar Amurka ta sakashi cikin wanda zata kawowa Khàrì

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Daya daga cikin manyan malaman Arewa ya bayyana cewa kasar Amurka ta sakashi cikin wanda zata kawowa Khàrì

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya bayyana cewa kasar Amurka ta sakashi cikin malaman da zata jefawa Bòm. Ya bayyana hakane a yayin karatun da yake a masallacinsa. Malam ya kara da cewa an kirashi a waya aka sanar dashi daga Abuja. Kasar Amurka ta kawo Khàrì jihar Sokoti inda tace tana fadane da masu Mhuzghunawa Kiristoci.
Kalli Bidiyon abinda Gwamnan Bauchi yawa shugaban karamar hukuma da ya zauna kujera daya da sarkin Bauchi

Kalli Bidiyon abinda Gwamnan Bauchi yawa shugaban karamar hukuma da ya zauna kujera daya da sarkin Bauchi

Duk Labarai
A wani Bidiyo da yake yawo a kafafen sada sumunta, An ga Gwamnan Bauchi, Sanata Bala Muhammad ya cewa wani da ya zauna a kusa da Me Martaba Sarkin Bauchi ya tashi. Gwamnan ya cewa wanda ya zauna din me zai sa ya zauna kujera daya da Sarkin Bauchi? Yacewa Sarkin yana wasa da kujerar Sarauta. https://twitter.com/i/status/2007746894899138776 Gwamnan ya fadi maganar cikin tsawa. Wasu dai sun ce Gwamnan bai kyautawa mutumin ba inda wasu ke bayyana cewa, shugaban karamar hukuma ne.
Bankunan Najeriya sun rufe rassa 229 saboda mutane sun rage zuwa

Bankunan Najeriya sun rufe rassa 229 saboda mutane sun rage zuwa

Duk Labarai
Wani Rahoto da babban bankin Najeriya, CBN ya fitar yace, Bankukan Najeriya sun rufe rassa 229 a fadin kasar saboda raguwar yawan mutanen dake zuwa bankunan. Rahotan yace yawanci mutane na zuwa POS ne dan cirewa ko saka kudi maimakon su shiga Banki. Rahoton ya kara da cewa, an saka kudi sau 5,373 a shekarar 2023 inda a shekarar 2024 kuma aka saka kudi sau 5,144 wanda hakan ke nuna cewa yawan kudaden da ake sakawa a Bankuna sun ragu.