Thursday, January 8
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: Tsohuwar jarumar fina-finan Hausa, Maryam Jankunne ta yi gargadin a daina Zhaghin Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Kalli Bidiyon: Tsohuwar jarumar fina-finan Hausa, Maryam Jankunne ta yi gargadin a daina Zhaghin Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Duk Labarai
Tsohuwar jarumar fina-finan Hausa, Maryam Jan Kunne ta gargadi masu zagin gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da su daina. Ta yi wannan maganane akan shirin komawar gwamnan zuwa jam'iyyar APC. Tace babu yanda za'a yi a raba tsakanin Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da Kwankwaso. https://www.tiktok.com/@maryamabubakar24/video/7591086809044536632?_t=ZS-92lsJNKQtOK&_r=1
Kalli Bidiyon: Bayani dalla-dalla kan dalilin da yasa aka kama Khalifa Sani Zaria

Kalli Bidiyon: Bayani dalla-dalla kan dalilin da yasa aka kama Khalifa Sani Zaria

Duk Labarai
Daya daga cikin daliban malamin Addinin Islama Sheikh Khalifa Sani Zaria da aka kama ya fito yayi bayani dalla-dalla kan dalilin da yasa aka kamashi. Yace Addu'a ce aka baiwa malam yayi, shine aka biyashi, wai shine aka kamashi dalilin kudin da aka bashi. Yace ina 'yan siyasa da suke satar kudade da yawa? Yace kuma shin laifin malam ne dan yayi addu'a an bashi kudi? Kalli Bidiyon jawabin a comment. https://www.tiktok.com/@yushauyahaya1998/video/7590877679688109330?_t=ZS-92ledgevc9I&_r=1
Ba za’a dauke wuta ba ko so daya a shekarar 2026>>Ministan Wutar Lantarki ya bayar da tabbaci

Ba za’a dauke wuta ba ko so daya a shekarar 2026>>Ministan Wutar Lantarki ya bayar da tabbaci

Duk Labarai
Ministan wutar lantarki, Mr Adebayo Adelabu ya bayar da tabbacin samar da tsayayyar wutar Lantarki a shekarar 2026. Me baiwa ministan Shawara game da sadarwa da hulda da jama'a, Mr Bolaji Tunji. Ne ya bayyana hakan ranar Juma'a a wata sanarwa da ya fitar. Yace hakan na kunshene a cikin sakon sabuwar Shekara inda yace Gwamnati zata mayar da hankali wajan samar da tsayayyar wutar lantarki ga gidaje da masana'antu.
An fara cirewa ‘yan Najeriya Haraji: Ji yanda wata mata ke kuka bayan da aka cire mata harajin Naira 487,500

An fara cirewa ‘yan Najeriya Haraji: Ji yanda wata mata ke kuka bayan da aka cire mata harajin Naira 487,500

Duk Labarai
Wata mata shahararriya a kafafen sadarwa me suna Raye ta koka da cewa an cire mata harajin naira 487,500 bayan da ta kashe Naira Miliyan 6.5 wajan sayayya. Wannan koke nata na zuwane kwanaki kadan bayan da Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa za'a fara cirewa mutane Haraji ranar 1 ga watan Janairu. Ta wallafa rasit din harajin da aka cire mata wanda ya dauki hankula sosai. Da yawan 'yan Najeriya dai na ta kokawa da maganar Harajin da Gwamnatin tarayya ta kawo.
Da Duminsa:Yayin da Abba ke shirin Komawa APC, Shi ma Kwankwaso an bayyana jam’iyyar da zai koma

Da Duminsa:Yayin da Abba ke shirin Komawa APC, Shi ma Kwankwaso an bayyana jam’iyyar da zai koma

Duk Labarai
!A yayin da shirye-Shirye suka yi nisa kan cewa, Abba Kabir Yusuf, gwamnan Kano da aka fi sani da Abba Gida-Gida na shirin komawa jam'iyyar APC. Shi kuma jagoran Tafiyar Kwankwasiyya, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso na shirin komawa jam'iyyar ADC. Kafar Thisday tace Kwankwaso na tattaunawa da jam'iyyar ADC inda yake shirin hadewa da su Atiku da Obi. Dama dai Atiku ne yazo na 2 inda Obi ya zo na 3, Kwankwaso kuma ya zo na 4 a zaben shugaban kasa na shekarar 2023 da ya gabata. Ana tsammanin idan wadannan manyan 'yan Adawa suka hade waje daya duk da cewa jam'iyya me mulki na da gwamnoni 28 zasu iya bata wuta.
Da Duminsa: Sabuwar Hular ‘yan Kwankwasiyya Reshen Abba ta fito wadda ke nuna goyon bayan shugaba Tinubu

Da Duminsa: Sabuwar Hular ‘yan Kwankwasiyya Reshen Abba ta fito wadda ke nuna goyon bayan shugaba Tinubu

Duk Labarai
'Yan kwankwasiyya Bangaren Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf sun fito da sabuwar Hula me nuna cewa suna tare da Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. An ga Jar Hular me dauke da Tambarin Tinubu a jiki tana yawo a kafafen sada zumunta. Hakan na zuwane yayin da Rahotanni suka ce ranar Litinin Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf zai koma jam'iyyar APC.
Kalli Bidiyon:Mahaifiyata bata yi Boko ba shiyasa idan an kai mata abinda nake sai in ce karyane>>Inji Soja Boy

Kalli Bidiyon:Mahaifiyata bata yi Boko ba shiyasa idan an kai mata abinda nake sai in ce karyane>>Inji Soja Boy

Duk Labarai
Tauraron mawakin Arewa, Soja Boy ya bayyana cewa, mahaifiyarsa bata yi Boko ba, shiyasa ma duk abinda aka kai mata yana yi sai yace mata karyane. Soja Boy yace duk 'yan uwansa yayi Blocking dinsu Mahaifiyarsa ce kadai ta rage yake magana da ita. Yace dalili suna ta gaya masa cewa abinda yake ba kyau. Yace akwai inda yake son kaiwa kuma zai kai kamin ya mutu zai daina. https://www.tiktok.com/@sojaboygarkuwayanarewa/video/7590765878594129163?_t=ZS-92lCSlKFAOX&_r=1
Da Duminsa: Matatar Man Dangote ta dakatar da aiki

Da Duminsa: Matatar Man Dangote ta dakatar da aiki

Duk Labarai
Rahotanni daga matatar man Dangote tace an dakatar da aiki a bangaren tace man fetur na matatar. Hakan na zuwane daga bakin mataimakin shugaban kamfanonin Dangote me suna Devakumar Edwin wanda yace an dakatar da aikinne dan wasu 'yan Gyare-Gyare. Yace idan aka kammala gyaran yawan man fetur din da matatar ke tacewa zai karu daga ganga 650,000 kullun zuwa ganga 700,000 kullun. Wannan dalili yasa tuni Depot dake sayarwa da 'yan kasuwa man fetur suka kara farashin man su zuwa Naira 800 akan kowace lita.