Rahotanni sun bayyana jihohin da Talakawa suka fi yawa a Najeriya.
Ga yankunan kamar haka:
1 North East — 37.9%2 North West — 29.6%3 North Central — 15.1%4 South East — 5.0%5 South South — 1.7%5 South West — 1.7%
Tauraruwar fina-finan Hausa, Maryam Yahya na ci gaba da daukar Hankula bayan da take ci gaba da sakin hotuna da Bidiyon ta babu rigar mama.
A baya dai ta rika shan suka duk da wasu na yabawa.
Hakanan a wannan karin ba wasu sun yaba inda wasu suka ci gaba da jawo hankalinta ta daina.
Kalli Bidiyon anan
Tauraron fina-finan Hausa, Saheer Abdul yayi karin haske kan labaran da ake yadawa cewa yana da mata 7.
Ya yi bayanin ne a hirar da Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon ta yi dashi a shirinta na Gabon Show dake YouTube.
Saheer yace shima haka ya ji wannan magana.
Yace amma ba gaskiya bane.
https://www.tiktok.com/@hadiza.gabon.tv/video/7565603415259155719?_t=ZS-90tsRoeXYIr&_r=1
Shugaban ƙasar Kamaru mai shekara 92 a duniya ya sake lashe zaɓen shugaban ƙasar a karo na takwas, bayan da Majalisar Kundin Tsarin Mulkin ƙasar ta ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen na ranar 12 ga watan Oktoba.
Biya ya lashe zaɓen ne bayan ya samu kashi 53.66% na ƙuri'un da aka kaɗa, yayin da babban abokin hamayyarsa Issa Tchiroma Bakary ya zo na biyu da kashi 35.19%, kamar yadda Majalisar ta bayyana.
"Paul Biya ya zama zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, bayan ya samu mafi yawa na ƙuri'un da aka kaɗa," in ji Clement Aatanga, shugaban Majalisar Kundin Tsarin Mulki ta ƙasar.
Kashi 57.76% ne na waɗanda suka cancanci kaɗa ƙuri'a suka fita domin yin zaɓen, inda kashi 42.24% suka ƙaurace.
Tsohon Gwamnan Jigawa, Sule Lamido yayi barzanar Kai jami'iyyarsa ta PDP kara kotu.
Sule Lamido ya bayyana hakane bayan kasa sayen Fom din tsayawa takarar shugaban jam'iyyar a ranar Litinin
Yace idan bai samu damar sayar fom din ba zai iya garzayawa kotu dan jin dalilin da yasa aka hanashi.
A baya dai, Sule Lamido ya bayyana aniyarsa ta son tsayawa takarar shugaban jam'iyyar PDP a shafinsa na Facebook.
Saidai wasu manya a jam'iyyar sun bayyana cewa, Kabiru Tanimu Turaki suke son tsayarwa a matsayin shugaban jam'iyyar
Tauraron mawakin Batsa, Soja Boy ya bayyana cewa yana sane cewa akwai iskanchi a wakokonsa.
Saidai yace dalilinsa na saka Iskanchi a wakokinsa shine, ya ga abinda mutane ke so kenan.
Yace kuma idan Babu Iyskanchi a waka mutane basa kallo.
https://www.tiktok.com/@maaunipodcast/video/7557035389358312722?_t=ZS-90th9EZljZg&_r=1
Tauraruwar fina-finan Hausa, Wadda ta bayyana kanta a matsayin shugabar matan Kannywood Rashida Mai Sa'a ta fito ta baiwa kabiru Legas Hakuri kan sawa da yayi 'yansanda suka kama Jarumar Kannywood, Khadija MaiNumfashi.
Rashida ta yi kira ga Kabiru da cewa, ya tuna da cewa soyayya ce ta hadashi da Khadija MaiNumfashi dan haka bai kamata ya wulakantata ba.
Tace ta yi magana da mahaifiyar Khadija dan a nemo mata lambar Kabiru Legas din amma duk da haka taga ya kamata ta yi Bidiyo dan ya gani.
https://www.tiktok.com/@backup_rashida_mai_saa/video/7565707358228319496?_t=ZS-90teTfTWgE5&_r=1
Malamin Addinin Islama, Malam Aminu Ibrahim Daurawa ya bayyana cewa, akwai wata mata da mijinta ya saketa ya bata Naira Miliyan 7 da Mota amma tace bata so.
Malam ya kara da cewa, Matar tace ya taimaka ya roki mijinta ya mayar da ita ya karbi kudinsa da motar daya bata ita dai tana son ci gaba da zama dashi ta mutu a gidansa.
Malam ya bayyana hakane a daya daga cikin karatuttukan da yake yi.
https://www.tiktok.com/@nurasara531/video/7565809192498367752?_t=ZS-90taIXPgUfB&_r=1
Attajirin Africa, Aliko Dangote a hukumance ya sanar da mayar da matatar man fetur dinsa ta rika fitar da ganga Miliyan 1.4 kullun Maimakon Ganga 650,000 da yake fitarawa a yanzu.
Yace hakan zai sa matatar tasa ta zama ta Daya a Duniya wajan yawan fitar da man fetur.
Dangi ya sanar da hakane a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai.
Ya godewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da kuma 'yan Najeriya bisa hadin gwiwar da suka bashi.