Saturday, February 14
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon: VDM ya bayyana ainahin abinda ya cuci a wasan da suka yi jiya da Morocco

Kalli Bidiyon: VDM ya bayyana ainahin abinda ya cuci a wasan da suka yi jiya da Morocco

Duk Labarai
Shahararren dan fafutuka, VDM ya bayyana ainahin abinda ya coci Najeriya a wasanta da Morocco a darwn jiya. VDM wanda yana cikin filin wasan da aka yi jiya a kasar Morocco. Yace abu na farko shine yawan magoya bayan Morocco. Yace akwai kuwan mutane dubu 60 a cikin filin wasan inda yace kuma 'yan Najeriya a ciki basu wuce mutane dubu 5. Yace da 'yan Najeriya sun dauki kwallo sai ka ji ana musu eho duk da dai sun yi kokarin samun karfin zuciyar buga wasan. yace wannan ya ci 'yan Najeriya a wasan na jiya. Hakanan ya dora Alhajin rashin nasarar akan Kocin Najeriya inda yace bai yi canjecanjen da suka kamata ba. Ya kuma bayyana cewa ya ji wasu 'yan kasar Morocco na cewa siyan Rafali aka yi. https://twitter.com/i/status/2011737120675610955
Kalli Bidiyon: Dan Najeriya da ya je kallon wasan Najeriya da Morocco a kasar Morocco yace ‘yan Najeriya a filin wasan basu wuce su 20 ba, da ace Najeriya taci Morocco da sun dandana kudarsu

Kalli Bidiyon: Dan Najeriya da ya je kallon wasan Najeriya da Morocco a kasar Morocco yace ‘yan Najeriya a filin wasan basu wuce su 20 ba, da ace Najeriya taci Morocco da sun dandana kudarsu

Duk Labarai
Wani dan Najeriya da ya je kasar Morocco kallon wasan Najeriya da Morocco ya dauki hankula bayan da yace duka 'yan Najeriya da suka je filin wasan basu wuce su 20 ba. Yace da Najeriya ta ci Morocco, da sun dandana kudarsu. https://twitter.com/i/status/2011684491723751586
Mawakin Najeriya, Davido ya tafka Asarar Naira Miliyan 495 a cacar da ya buga cewa Najeriya ce zata yi nasara a wasanta da Morocco

Mawakin Najeriya, Davido ya tafka Asarar Naira Miliyan 495 a cacar da ya buga cewa Najeriya ce zata yi nasara a wasanta da Morocco

Duk Labarai
Shahararren mawakin Najeriya, Davido ya bayyana cewa ya tafka asarar Naira Miliyan 495 saboda cacar da ya buga akan cewa Najeriya ce zata ci Morocco. Davido dai wanda yayi suna wajan yin caca da son kwallo, ya saka cewa, Najeriya ce zata ci amma sai Morocco ta yi nasara. Davido ya wallafa rasit din cacar da yayi a shafinsa na sada zumunta.
Ji abinda Mataimakin Gwamnan Kano, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo yayi kan komawar Abba Kabir Yusuf APC da ya jawo masa yabo

Ji abinda Mataimakin Gwamnan Kano, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo yayi kan komawar Abba Kabir Yusuf APC da ya jawo masa yabo

Duk Labarai
Mataimakin Gwamnan jihar Kano, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo ya bayyana goyon baya ga Kwankwaso a bayyane a yayin da Gwamna, Abba Kabir Yusuf ke shirin komawa APC. An ga Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo a gidan Kwankwaso ranar Laraba a yayin da wasu 'yan kwankwasiyyar suka kaiwa Kwankwaso ziyara a gidansa dake Kano. Ya zauna a kusa da Kwankwaso yayin ganawar wanda da yawa 'yan Kwankwasiyya suka bayyana cewa hakan alamar nuna yana tare da Kwankwaso ne.
Gwamnatin tarayya ta sanar da sabon harajin VAT da ‘yan Najeriya masu amfani da banki zasu biya

Gwamnatin tarayya ta sanar da sabon harajin VAT da ‘yan Najeriya masu amfani da banki zasu biya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bukaci bankuna su fara karbar sabon Harajin VAT na kaso 7.5 akan duk wani amfani da masu hulda da banki suke yi. Za'a rika cire harajinne akan aika kudi, karbar katin ATM, duba balance da sauransu. Kuma Harajin zai fara aiki ne nan da ranar 19 ga watan Janairu, watau Ranar Litinin me zuwa. Tuni dai bankunan suka aikawa masu hulda dasu sanarwar fara karbar Haraji.