Friday, March 6
Shadow

Duk Labarai

Gwamnatin tarayya ta kayyade shekaru 12 a matsayin shekarun shiga ajin karamar sakandare na JSS1

Gwamnatin tarayya ta kayyade shekaru 12 a matsayin shekarun shiga ajin karamar sakandare na JSS1

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta kayyade shekaru 12 a matsayin shekarun shiga ajin karamar sakandare na JSS1. Hakan na kunshene a bayanan da gwamnati ta fitar kan yanda makarantun kudi zasu riga gudanar da harkar ilimi. Sanarwar tace yaro sai ya kai shekara 3 sannan za'a sakashi a ajin Nursery 1 Sannan idan ya kai shekaru 4 a sakashi a ajin Nursery 2. Gwamnati tace kamin yaro ya fara ajin farko na primary watau Primary one sai ya kai shekaru 6. Dan haka kowane yaro sai ya kai shekaru 6 yana karatun Primary daidai lokacin da zai kammala Primary, ya zamana yana da shekaru 12. Dokar tace a daidai lokacin da yaro zai kammala sakandare zai kasance yana da shekaru 18 kenan.
Ga ‘Yan Najeriya na fama da yunwa, ga rikici tsakaninka da Kashim Shettima amma jam’iyyar mu ta ADC ce ta tsone maka ido>>Atiku ga Shugaba Tinubu

Ga ‘Yan Najeriya na fama da yunwa, ga rikici tsakaninka da Kashim Shettima amma jam’iyyar mu ta ADC ce ta tsone maka ido>>Atiku ga Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya mayarwa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu martani kan sukar da shugaban kasar yayi ga jam'iyyar ADC. Shugaba Tinubu a wajan taron jam'iyyar APC inda aka zabi sabon shugaban jam'iyyar ya bayyana cewa mutanen jam'iyyar ADC rikitattun mutanene. Saidai a martaninsa, Atiku yace akwai abubuwa da yawa da ya kamata Shugaba Tinubu ya mayar da hankali kansu maimakon sukar jam'iyyar ADC wanda ya mayar abin yi kullun. Yace tattalin arzikin Najeriya na cikin halin ni 'yasu, 'yan Najeriya na cikin yunwa, sannan ga rikici tsakaninshi da mataimakinsa, Kashim Shettima wadannan abubuwan ya kamata ya mayar da hankali kansu ba sukar jam'iyyar ADC ba.
Dan kudu zamu tsaida takarar shugaban kasa a 2027>>Inji Jam’iyyar PDP

Dan kudu zamu tsaida takarar shugaban kasa a 2027>>Inji Jam’iyyar PDP

Duk Labarai
Jam'iyyar PDP ta sanar da cewa, dan kudu zata tsayar takarar shugaban kasa a shekarar 2027. Jam'iyyar ta bayyana hakane a zaman masu ruwa da tsaki da ya wakana a jiya. Sannan ta canja wajan da zata gudanar da taronta na zaben shuwagabannin jam'iyyar wanda a da za'a yi a Kano, yanzu a jihar Oyo za'a yi. Ana zargin an yi hakanne dan shiryawa gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinda hanya a shirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2027. Saidai hakan kuma zai zama koma baya ga Nyesom Wike wanda tuni dangantaka tsakaninsa da Gwamna Makinde ta yi tsami.
Kalli Bidiyon: Yanda Shugaba Tinubu yayi subutar baki yace tsohon shugaban APC Dr. Rabiu Ganduje

Kalli Bidiyon: Yanda Shugaba Tinubu yayi subutar baki yace tsohon shugaban APC Dr. Rabiu Ganduje

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi subutar baki inda yace tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dr. Rabiu Ganduje. Shugaban na son yace tsohon shugaban jam'iyyar APC Dr. Abdullahi Umar Ganduje ne a wajan wani taro. Wasu dai Sun ce kwankwaso ne a ransa shiyasa. https://www.tiktok.com/@comr._aliyu_ak_balarabe/video/7530686949414276357?_t=ZM-8yJmcICu4iE&_r=1 Lamarin ya dauki hankula.
Kalli Bidiyo da Duminsa Yanda aka saka gawa a kabari, amma kabarin ya ki karbarta a makabartar Bashama dake Kaduna, hankula sun tashi

Kalli Bidiyo da Duminsa Yanda aka saka gawa a kabari, amma kabarin ya ki karbarta a makabartar Bashama dake Kaduna, hankula sun tashi

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kaduna na cewa, Kabari ya ki karbar gawar wata mata da ta rasu. Rahoton yace lamarin ya farune a Makabartar Bashama dake Tudun Wada Kaduna. A Bidiyon an ga hadda mata nata tururuwar zuwa ganin abinda ya faru cikin makabartar Saidai wasu da yawa sun musanta faruwar lamarin: https://www.tiktok.com/@amaryamerabo3/video/7530771752314555655?_t=ZM-8yJlmQQiYbw&_r=1 Rahotan dai yace lamarin jita-jitane.
Kalli Bidiyon: Idan na chire kaya na yi Tumbur a gaban su Gfresh da Mai Wushirya, sai su yi ta kokarin yin Alfasha dani, Addu’a ce ke kareni>>Inji Murja Kunya

Kalli Bidiyon: Idan na chire kaya na yi Tumbur a gaban su Gfresh da Mai Wushirya, sai su yi ta kokarin yin Alfasha dani, Addu’a ce ke kareni>>Inji Murja Kunya

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Tauraruwar Tiktok, Murja Kunya ta bayyana cewa, Abokanta su Gfresh da Mai Wushirya duk kwarata ne. Ta ce sukan kai mata harinnyin fyade amma Allah sai ya taimaketa ta tsalake. inda ta alakanta hakan da cewa Addu'a ce ke kareta. https://www.tiktok.com/@murjakunya0/video/7530359461790092551?_t=ZM-8yJjHylG3Uu&_r=1
Munci mun lashe zaben 2027, babu wani da zai iya hanamu>>Sabon Shugaban APC, Farfesa

Munci mun lashe zaben 2027, babu wani da zai iya hanamu>>Sabon Shugaban APC, Farfesa

Duk Labarai
Sabon shugaban jam'iyyar APC, Farfesa Nentawe Yilwatda ya bayyana cewa, jam'iyyar tasu taci ta lashe zaben shugaban kada na shekarar 2027. Ya bayyana hakane bayan da aka rantsar dashi a jiya. Farfesa Nentawe Yilwatda yace a karkashin shugabancinsa, za'a ga karin shigar manyan 'yan siyasa jam'iyyar APC. Ya sha Alwashin mayar da jam'iyyar APC jam'iyya abin Alfahari ga Najeriya baki daya.
Da Duminsa: Sarkin Gusau ya rigamu gidan Gaskiya

Da Duminsa: Sarkin Gusau ya rigamu gidan Gaskiya

Duk Labarai
Rahotanni da muke samu na cewa, Allah yawa Me martaba Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello rasuwa. Ya rasu yau, Juma'a a Abuja bayan jinya. Hutudole ya fahimci cewa, Sarkin ya rasu yana da shekaru 71 a Duniya. Ya zama sarki ne a ranar 16 ga watan Maris na shekarar 2015 bayan rasuwar mahaifinsa. Kakakin Gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Idis ya tabbatar da rasuwar Sarkin inda ya mika sakon ta'aziyya.