Tuesday, May 12
Shadow

Duk Labarai

Ku yi hattara da abinda kuke dorawa a kafafen sadarwa, yanzu Haka Gwamnati ta kulle shafuka Miliyan 13 da suka dora abubuwan da basu dacw ba a Soshiyal Midiya

Ku yi hattara da abinda kuke dorawa a kafafen sadarwa, yanzu Haka Gwamnati ta kulle shafuka Miliyan 13 da suka dora abubuwan da basu dacw ba a Soshiyal Midiya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta sanar da kulle shafukan yanar gizo guda Miliyan 13 saboda dora abubuwan da basu dace ba. An kulle shafukan ne dake kan TikTok, Facebook, Instagram, and X, bayan da wadannan kafafe suka bada hadin kai wa Gwamnatin Najeriya wajan kai rahoton irin wannan shafukan. Wadannan shafukan sun sabawa dokar Najeriya wadda hukumomin Nigerian Communications Commission (NCC), the National Information Technology Development Agency (NITDA), da the National Broadcasting Commission (NBC) suka samar ta amfani da kafafen sada zumunta. Rahoton yace an goge shafukan ne dan tabbatar da ana tsaftace irin abubuwan da ake yadawa a kafafen sada zumunta. Wakiliyar Gwamnatin tarayya, Hajiya Umar ta jinjinawa kamfanonin sadarwar saboda bada hadin kai wajan goge irin wadannan shafukan.
Kalli Bidiyon yanda Ummi Nuhu ta yi kyau kwanaki kadan bayan da Hadiza Gabon ta yi hira da ita

Kalli Bidiyon yanda Ummi Nuhu ta yi kyau kwanaki kadan bayan da Hadiza Gabon ta yi hira da ita

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wani Bidiyon Ummi Nuhu ya bayyana inda aka ganta daya daga cikin masu shirya fina-finai yana hira da ita inda aka ga ta yi haske. A baya dai a lokacin da Hadiza Gabon ta yi hira da ita An ga Ummi Nuhu a wani hali na ban tausai inda daga baya rahotanni suka ce an hada mata kudaden tallafi. https://www.tiktok.com/@yakubu_producer/video/7539112872220101909?_t=ZS-8z2OYE8MRw8&_r=1 Da yawa dai sun yi mamakin ganin wannan Bidiyon inda suke tambayar shin sabon Bidiyon ne?
Abin Kunya: Kalli yanda aka bar Gurin da aka warewa Najeriya a taron kasashe dake gudana a Birnin Tokyo na kasar Japan ba kowa, yayin da sauran kasashen Duniya suke tsaye a wajen nasu

Abin Kunya: Kalli yanda aka bar Gurin da aka warewa Najeriya a taron kasashe dake gudana a Birnin Tokyo na kasar Japan ba kowa, yayin da sauran kasashen Duniya suke tsaye a wajen nasu

Duk Labarai
Wani dan Najeriya me suna Idris Ayo Bello ya bayyana yanda da ya halarci wajan taron ci gaban Afrika da aka gudanar a birnin Tokyo na kasar Japan da kuma abin kunyar da ya gani. Yace wajan da aka warewa Najeriya ta tsaya babu kowa a wajan. Yace da ya ga abin yayi yawa, shine da kansa ya je wajan ya tsaya ya kuma rika amsa tambayoyi akan kasuwancin Najeriya da ci gabanta da wasu 'yan kasashe ke yi. Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dai ya halarci wajan taron, kuma rahotanni sun bayyana cewa, an tanadi mutanen da zasu tsaya a irin wannan waje dan wakiltar Najeriya.
EFCC zata fara binciken tsohon shugaban NNPCL, Mele Kolo Kyari kan zargin satar Dala Biliyan $7.2 na gyaran matatun man fetur

EFCC zata fara binciken tsohon shugaban NNPCL, Mele Kolo Kyari kan zargin satar Dala Biliyan $7.2 na gyaran matatun man fetur

Duk Labarai
Hukumar hana yiwa tattalin arziki kasa zagon kasa, EFFC ta bayyana cewa, zata fara binciken tsohon shugaban NNPCL, Mele Kolo Kyari kan zargin satar Dala Biliyan $7.2 na gyaran matatun man Najeriya. Hakan na zuwane bayan da tuni kotu ta kulle asusun ajiyarsa na banki guda 4 dake dauke da makudan kudade. Rahoton Daily Trust yace tuni aka fara binciken wasu na kusa da Kyari inda EFCC tace tana son samun isassun bayanai akanshi kamin ta fara bincikenshi. Game da cewa, Kyari baya Najeriya, Hukumar tace wannan ba matsala bane da zarar sun bukaci kamashi ko bincikenshi kamashi ba abune me wuya ba.
Dan majalisar dokoki na majalisar jihar Nasarawa, Musa Gude ya dauki hankula saboda nada masu taimaka masa guda 106

Dan majalisar dokoki na majalisar jihar Nasarawa, Musa Gude ya dauki hankula saboda nada masu taimaka masa guda 106

Duk Labarai
Dan majalisar wakilai na majalisar jihar Nasarawa, Musa Gude ya nada masu taimaka masa guda 106. Ya bayyana hakane a hirar da yayi da kamfanin dillancin labaran Najeriya, NAN inda yace ya nada mutane 106 a matsayin masu taimaka masa ne dan ya tallafawa rayuwarsu. Yace daga ciki akwai wadanda yake biya albashin Naira Dubu 10 har zuwa Dubu 100. Dan majalisar wanda a jam'iyyar SDP yake daga mazabar Uke/Karshi yace ya tallafawa mutane a bangarori daban-daban da suka hada da Noma, ilimi, da sauransu.
Zamu Tùbè kayan mu, mu yi Tumbur mu nuna komai mu yi zànga-zànga tsyrara idan ba a daina rushe mana gidaje ba>>Inji Matan Legas

Zamu Tùbè kayan mu, mu yi Tumbur mu nuna komai mu yi zànga-zànga tsyrara idan ba a daina rushe mana gidaje ba>>Inji Matan Legas

Duk Labarai
Mata a birnin Legas sun yi barazanar yin zanga-zangar tsirara dan tursasa daina rushe musu gidaje. Matan daga yankin Ilaje sun yi zanga-zangar lumana zuwa majalisar dokokin jihar ta Legas inda suka nemi taimakon gwamnan jihar, Babajide Sonwo Olu da kakakin majalisar Dokokin jihar,Mudashiru Obasa su saka baki a daina rushe musu gidaje. Sun zargi sarakunan gargajiyarsu da yi musu kwacen gidaje. Daya daga cikin matan wadda dattijuwa ce, ta fito inda take barazanar cewa, zasu yi zanga-zanga tsirara idan ba a daina rushe musu gidaje ba. Shima shugaban mazauna yankin na Ilaje, Rafael Irowainu ya bayyana cewa wasu sarakuna na amfani da sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu suna rushe gidaje dan su yi gine-gine. Ya kara da cewa, amma basu yadda shugaba ne ya aika mutanen ba.