Sunday, February 15
Shadow

Duk Labarai

NNPP tace ba zata baiwa Kwankwaso takara a 2027 ba

NNPP tace ba zata baiwa Kwankwaso takara a 2027 ba

Duk Labarai
Jam'iyyar NNPP ta bayyana cewa, ba zata baiwa Dr. Rabiu Musa Kwankwaso takara a zaben shekarar 2027 ba. Jam'iyyar ta bayyana hakane ta bakin sakataren ta, Mr. Ogini Olaposi a sanarwar da ya fitar ranar 12 ga watan Janairu. Ya bayyana cewa jam'iyyar zata baiwa asalin 'yan jam'iyyar masu kishinta takara ne. Hakan na zuwane biyo bayan rashin jituwar da aka samu tsakanin Kwankwaso da jam'iyyar ta NNPP.
Kalli Bidiyon: Adam A. Zango ya bayyana cewa zai sakawa Mataimakin shugaban kasa da wani abu da shi Kashim Shettima ba zai iyawa kansa ba

Kalli Bidiyon: Adam A. Zango ya bayyana cewa zai sakawa Mataimakin shugaban kasa da wani abu da shi Kashim Shettima ba zai iyawa kansa ba

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa Adam A zanga ya baayyana cewa, zai sakawa Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima da ya bashi kyautar mota da wani abu da shi Kashim din ba zai iyawa kansa ba. Ya bayyana hakane yayin sakon Godiya daya fitar ga Kashim Shettima inda yace kuma yana godewa masoyansa. https://www.tiktok.com/@og_adam_a_zango_official/video/7594141203805785364?_t=ZS-92zhZA23lx3&_r=1
Wani Bincike ya gani masa da suka fito daga kauye da kuma ke fama da talauci da yunwa sun fi son mata masu manyan Nònùwà

Wani Bincike ya gani masa da suka fito daga kauye da kuma ke fama da talauci da yunwa sun fi son mata masu manyan Nònùwà

Duk Labarai
Wani bincike da aka wallafa a PLOS ONE wanda masana suka tabbatar da sahihancinsa yace maza da suka fito daga kauye sannan matalauta kuma masu fama da yunwa sun fi son mata masu manyan Nonuwa. Hakanan a bangare guda kuma mazan da suke da dukiya da koshi sun fi son mata masu kana na da matsakaitan nonuwa. Masana ilimin halayyar dan adam Viren Swami da Martin J. Tovée ne suka gudanar da wannan binciken. Sannan sun gudanar da wannan bincikenne a kasashen Ingila da Malaysia. Sun samu maza 266 daga kauyuka sannan mata lauta sannan kuma aka samu wasu mazan masu kudi. Kowanne daga cikinay an nuna musu mataye masu manyan nonuwa da masu matsakaita da masu kananan nonuwa. Sakamakon binciken ya nuna cewa, maza da suka fito daga kauye sannan suke fama da Talauci sun fi son mata masu ...
Kalli Bidiyon: Wata ‘yar Najeriya dake zaune a kasar Amurka ta nuna wani bangare na kasar Amurkar da ya dauki hankula sosai

Kalli Bidiyon: Wata ‘yar Najeriya dake zaune a kasar Amurka ta nuna wani bangare na kasar Amurkar da ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Wata 'yar Najeriya dake zaune a kasar Amurka, ta nuna wani sashe na kasar Amurka da tace mutane basu yi tsammanin gani ba. A yayin da a fina-finan kasar Amurka ake nuna ginegine masu tsawo da kuma gidaje masu kyau. A Bidiyon nata an ga wata unguwar Talakawa data nuna. https://www.youtube.com/watch?v=WMaLJdebWsw?si=NX0q98YYH6zOhtcp
Kalli Bidiyon: Wike yayi martani kan kiran da ake cewa, shugaba Tinubu ya saukeshi daga Ministan Abuja

Kalli Bidiyon: Wike yayi martani kan kiran da ake cewa, shugaba Tinubu ya saukeshi daga Ministan Abuja

Duk Labarai
Ministan babban Birnin Tarayya, Abuja, Nyesom Wike yayi martani game da neman a saukeshi daga mukaminsa. Yace masu kiraye-kirayen su kwantar da hankalinsu wanda ya nasashi ne ke da wannan ikon, idan yaga cewa baya aikata abinda ya dace, to shine zai saukeshi. Ya kara da cewa amma shi yasan yana yin abinda ya kamata a matsayin Ministan Abuja. https://twitter.com/i/status/2010368170335305951
Wata Sabuwa: An baiwa Shugaba Tinubu shawarar yayi kokari tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya koma APC in ba haka ba zai kawo mai tangarda a zaben 2027

Wata Sabuwa: An baiwa Shugaba Tinubu shawarar yayi kokari tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya koma APC in ba haka ba zai kawo mai tangarda a zaben 2027

Duk Labarai
Dan takarar Gwamnan jihar Kebbi a jam'iyyar APC, Mallam Salihu Isa Nataro ya baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu shawarar ya yi kokarin mayar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai jam'iyyar APC. Yace masa, El-Rufai na da karfin fada aji sosai musamman a siyasar Arewa maso yamma. Yace kuma komawarsa jam'iyyar APC zata sa talakawa da yawa su dawo suna son Tinubu din. Yace kada a bari rashin jituwa tsakanin shuwagabannin jam'iyya da El-Rufai yasa a kyaleshi. Ya bayyana cewa ya kamata a yi kokari El-Rufai ya koma APC kamin zaben 2027.