Rashin Wutar Lantarki na Kwanki 10 a jihar Kano ya gurgunta harkokin tattalin arzikin jihar inda Cajin waya yanzu ana karbar Naira 200, jarkar ruwa ma ta koma Naira 200
Rashin tsayayyiyar wutar lantarki na tsawon lokaci na sama da kwanaki 10 ya jawo dakatar da kasuwanci a cikin ƙwaryar birnin Kano da kewaye.
Wasu mazauna Kano da suka zanta da kamfanin dillancin labarai na ƙasa (NAN) a ranar Lahadi, sun koka game da rashin sanin tabbacin abin da za su yi bayan faɗuwar babban layin wutar lantarki wanda ya jefa al’umma cikin duhu da shafar kasuwanci da al’umma a gidajensu.
Da yawa daga cikin ‘yan kasuwa sun koka game da illar rashin wuta ga kasuwancinsu.
Wani mai gidan otel da unguwar Sabon Gari da ke ƙaramar hukumar Fage, Jude Michael, ya ce yana cikin tashin hankali.
Michael ya ce ya rasa kwastamominsa sakamakon rashin wuta da yake amfani da ita wajen ajiye kayan abin sha.
“Na shafe tsawon kwanaki ina aiki da Janareta kuma har ya fara taɓa k...








