Thursday, February 19
Shadow

Duk Labarai

Kalli Bidiyon yanda wani dan kasar China ya yayyaga kudin Naira saboda jin haushin an kulle masa kamfaninsa a Legas

Kalli Bidiyon yanda wani dan kasar China ya yayyaga kudin Naira saboda jin haushin an kulle masa kamfaninsa a Legas

Duk Labarai
Wani dan kasar China a birnin Legas ya wulakanta takardar Naira saboda hukumomi a jihar ta Legas sun kulle kamfaninsa saboda karya wasu dokoki. Lamarin dai ya farune a kan hanyar Lekki-Epe expressway. https://twitter.com/dipoaina1/status/1856954344744137159?t=QDPRjD88-AWJzbxnaqQTyA&s=19 Tuni dai Bidiyon ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda da dama ke kiran ya kamata a hukuntashi.
Kasar Iran ta samar da gidan mahaukata dan kai matan dake kin saka hijabi a kasar

Kasar Iran ta samar da gidan mahaukata dan kai matan dake kin saka hijabi a kasar

Duk Labarai
Kasar Iran ta samar da gidan mahaukata a babban birnin kasar, Tehran inda za'a rika kai mata dake kin saka Hibaji dan kula dasu. An dai sakawa asibitin sunan Clinic for Quitting Hijab Removal, tun a shekarar 2022 ne dai kasar ke fama da masu fafutuka dan ganin an daina tursasa sanya Hijabi a kasar. Jami'ar da zata rika kula da wannan asibiti me suna Mehri Talebi Darestani tace an budeshine musamman saboda koyawa yara mata kyan al'adarsu da kuma muhimmancin hakan a addinin Musulunci.
Kasar Nijar ta koro ‘yan Najeriya 148 da suka shigar mata kasa ba bisa ka’ida ba

Kasar Nijar ta koro ‘yan Najeriya 148 da suka shigar mata kasa ba bisa ka’ida ba

Duk Labarai
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA ta bayyana cewa ta karbi 'yan Najeriya su 148 da kasar Nijar ta dawo dasu gida saboda shiga kasarta ba bisa ka'ida ba. Hukumar tace ranar Talatace aka dawo da 'yan Najeriyar a filin jirgin sama na Murtala Muhammad dake Legas. Hukumar tace 120 daga cikinsu maza ne manya inda guda 9 mata ne manya sai, sai guda 10 yara ne maza, sai 7 yarane mata, sai jarirai 2.
Magidanci ya yi karyar cewa an yi garkuwa dashi bayan da ya ranci kudi Naira Miliya 1 ya buga caca dasu aka cinye kudin

Magidanci ya yi karyar cewa an yi garkuwa dashi bayan da ya ranci kudi Naira Miliya 1 ya buga caca dasu aka cinye kudin

Duk Labarai
Wani magidanci daga jihar Ogun, Enitan Awoyemi dan kimanin shekaru 41 ya buga caca inda aka biyoshi bashin Naira Miliyan daya. Ganin cewa ba zai iya biyan kudin ba ne yayi karyar cewa an yi garkuwa dashi inda ya kira matarsa ya gaya mata. Matar ta kira jami'an tsaron Amotekun inda suka fara bincike. Kwamandan Amotekun din a jihar, Brigadier General Alade Adedigba (retd.) Ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace sun gano cewa, Enitan karya yayi ba'a yi garkuwa dashi ba. Yace sun ganoshi yana kokarin kashe kansa inda yace ya sha maganin kwari amma sun kaishi asibiti idan ya warke zasu mikashi wajan 'yansanda.
Hotuna: Gawar marigayi shugaban sojojin Najeriya, Lagbaja ta isa Legas

Hotuna: Gawar marigayi shugaban sojojin Najeriya, Lagbaja ta isa Legas

Duk Labarai
Rahotanni daga Legas na cewa, gawar marigayi shugaban sojoji, Lt. Gen. Taoreed Lagbaja ta isa Jihar inda za'a yi jana'izarsa. Gawar ta sauka a filin jirgin sama na Murtala Muhammad dake Legas din da safiyar ranar Alhamis. A ranar Larabar data gabata ne dai gwamnatin tarayya ta tabbatar da mutuwar shugaban sojojin. Hukumar sojojin Najeriya ta sanar da cewa ranar November 15, 2024 za'a yi jana'izar marigayin a makabartar sojoji dake Abuja
Sojojin Najeriya sun soma fatattakar Làkùràwà daga sassan jihar Kebbi

Sojojin Najeriya sun soma fatattakar Làkùràwà daga sassan jihar Kebbi

Duk Labarai
Rundunar sojin Najeriya ta ƙaddamar da hare-hare kan ƙungiyar 'yanbindiga ta Lakurawa da ta ɓulla a wasu sassan jihohin Kebbi da Sokoto na arewa maso yammacin ƙasar. Rahotanni daga yankin ƙaramar hukumar Augie na jihar Kebbi, sun ce sojojin ƙasar sun shiga wuraren da 'yan ƙungiyar suka kakkafa sansanoni tare da lalata su. Sojojin sun kuma kori Lakurawan a dazukan ƙaramar hukumar, tare da kuɓutar da wasu daga cikin dabbobin da masu gwagwarmaya da makaman suka sace. Matakin na zuwa ne ƙasa da mako ɗaya da 'yan ƙungiyar suka yi artabu da mutanen gari Mera na yankin ƙaramar hukumar, tare da kashe mutum 15 da sace shanu masu yawa. Shugaban ƙaramar hukumar Augie, Hon Yahaya Muhammad Augie, ya shaida wa BBC cewa bayan dakarun ƙasar sun soma ƙaddamar da hare-hare kan ƙungiyar, yanzu ha...
Kalli Bidiyo: Matashi da ya kammala karatun Digiri daga jami’ar Umar Musa ‘Yar’Adua da sakamakon Digiri mafi daraja watau First Class na tallar Ruwa a Titin Abuja

Kalli Bidiyo: Matashi da ya kammala karatun Digiri daga jami’ar Umar Musa ‘Yar’Adua da sakamakon Digiri mafi daraja watau First Class na tallar Ruwa a Titin Abuja

Duk Labarai
Wani matashi me suna Ishaq dake sayar da ruwa wanda aka fi sani da Pure Water a Abuja ya bayyana cewa yana da kwalin kammala Digiri mafi daraja watau First Class. Matashin an yi hira dashi ne inda bidiyon hirar ta watsu sosai a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/Ummieey_k/status/1856821597476184530?t=eH65h9aWtgN1D3gr8mPRrA&s=19 Yace tun da ya kammala karatun bashi da aikin yi. Saidai Tuni wata baiwar Allah ta bukaci da a nemo mata shi dan ta taimaka masa.
Hukumar yaki da rashawa da cin hanci ICPC ta gurfanar da tsohon dan majalisa a kotu bisa zargin satar Naira Miliyan 18 inda kotu ta bayar da belinsa akan Naira miliyan 20

Hukumar yaki da rashawa da cin hanci ICPC ta gurfanar da tsohon dan majalisa a kotu bisa zargin satar Naira Miliyan 18 inda kotu ta bayar da belinsa akan Naira miliyan 20

Duk Labarai
Hukumar yaki da rashawa da cin hanci ICPC ta kama tsohon dan majalisar tarayya daga jihar Benue John Dyegh bisa zargin cin hancin Naira Miliyan 18 inda ta gurfanar dashi a kotu. Dan majalisar wanda ya wakilci mazabar Gboko/Tarka daga jihar Benue ya gurfana a gaban babbar kotun tarayya dake babban birnin jihar Makurdi ranar Litinin. Kakakin ICPC, Demola Bakare a sanarwar da ya fitar ranar Talata yace John a ranar May 19, 2014, ya karbi kudi da suka kai N18,970,000. Yace kudin na aikin gina makaranta ne a karamar hukumar Guma amma aka karkatar dasu zuwa asusun bankin wani kamfani me suna Midag Limited wanda John ke da hannu jari me yawa a ciki. Hakan ya sabawa dokar aikin gwammati. Mai Shari'a na kotun,Justice Abubakar ya bukaci a aika da John gidan yarin dake Makurdi har sai ...