Thursday, February 19
Shadow

Duk Labarai

Kasar Amurka ta ki yadda ta bayar da bayanai akan rayuwar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda tace wakilintane dake taimaka mata wajan cimma burikanta

Kasar Amurka ta ki yadda ta bayar da bayanai akan rayuwar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda tace wakilintane dake taimaka mata wajan cimma burikanta

Duk Labarai
A yayin da aka shigar da wata kara a kotun kasar Amurka ake neman bayanai game da rayuwar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a baya inda ake zargin ya yi ta'ammuli da kwaya da kuma maganar ingancin takardun karatunsa, kasar Amurka tace ba zata bayar da wadannan bayanai ba. Dan jarida, David Hundeyin ne ya shigar da kara yake neman bayanai akan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kuma tun a shekarar data gabatane dai kotun kasar Amurka ta ki yadda ta bayar da bayanan da yake nema. Dan jaridar yace hukumomin kasar Amurka, CIA, FBI, da DEA sun shigar da kara inda suma suke neman cewa kada a bashi bayanai akan shugaban kasar Bola Ahmad Tinubu inda CIA wadda kungiyar leken Asiri ce ta kasar Amurka tace Bola Ahmad Tinubu wakilinta ne da take amfani dashi wajan cimma muradunta. Zuwa yanzu dai...
Na karbi mulki Najeriya na cikin wahala da matsin tattalin arziki shiyasa na dage dan kawo gyara>>Shugaba Tinubu

Na karbi mulki Najeriya na cikin wahala da matsin tattalin arziki shiyasa na dage dan kawo gyara>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, ya karbi mulkin Najeriya a yayin da take cikin wahalar rashin tabbas na tattalin arziki. Shugaban yace shiyasa ya dauki matakai tsaurara musamman a bangaren kudi dan ganin ya kawo ci gaba. Shugaban ya bayyana hakane a wajan rantsar da zababben gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo inda mataimakinsa, Kashim Shettima ya wakilceshi. Yace a yanzu saboda matakan da ya dauka, kasar ta dauki hanyar ci gaba da nasara.
Mutane 243,000 sun daina biyan kudin talabijin ta DSTV a Najeriya saboda tsadar rayuwa

Mutane 243,000 sun daina biyan kudin talabijin ta DSTV a Najeriya saboda tsadar rayuwa

Duk Labarai
Rahotanni sun nuna cewa mutane 243,000 sun daina biyan kudin DSTV da GoTV saboda tsada rayuwa. Kamfanin wanda na kasar Afrika ta kudu ne ya bayyana cewa ya rasa wadannan mutanen ne daga watan Afrilu na wannan shekare zuwa watan Satumba na shekarar. An ga hakanne a cikin bayanan yanda kamfanin ya gudanar da kasuwancinsa wanda ya fitar a karshen watan Satumba. Kamfanin ya alakanta hakan da tsadar rayuwa wadda ta hana da tsadar kayan abinci, wutar lantarki, da man fetur. Kamfanin ya kara da cewa, ya rasa mitane 566,000 a gaba dayan nahiyar Afrika wanda suka daina biyan kudin DSTV da GoTV din.
Shugaba Tinubu ya dawo Abuja

Shugaba Tinubu ya dawo Abuja

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Abuja daga kasar Saudiyya inda ya je wajan taron kasashen Musulmai. Jirgin na shugaba Tinubu ya sauka ne da misalin karfe 8 na darennan a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe International airport. Manyan jami'an gwamnati ne suka mai maraba bayan saukarsa.
Kungiyoyin fafutuka 51 sun nemi EFCC ta kama shugaban jam’iyyar APC Ganduje kan zargin Rashawa da Cin Hanci, an samu Shaidu 143 zasu bayar da shaida akan cewa ya aikata laifin

Kungiyoyin fafutuka 51 sun nemi EFCC ta kama shugaban jam’iyyar APC Ganduje kan zargin Rashawa da Cin Hanci, an samu Shaidu 143 zasu bayar da shaida akan cewa ya aikata laifin

Duk Labarai
Kungiyoyin fafutuka 51 dake ikirarin yaki da rashawa da cin hanci sun nemi hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC ta kama shugaban jam'iyyar APC, Dr. Umar Abdullahi Ganduje kan zargin Rashawa da cin Hanci. Kungiyoyin sun rubuta takardar neman a kama Gandujene ranar November 4, 2024 inda ita kuma hukumar EFCC ta karbi takardar ranar November 7, 2024. A lokacin da yake rike da mukamin gwamnan Kano,an zargi Dr. Umar Abdullahi Ganduje da cin hanci da rashawa ta fannoni daban-daban. Akwaidai shaidu 143 wadanda suke a shirye su bayar da shaida akan zargin cin hanci da rashawa na Ganduje wadanda suka hada da ma'aikatan kananan hukumomi da 'yan canji da tsaffin ma'aikatan banki. Shuwagabannin kungiyoyin fafutukar da suka kai wadannan bukatu sun hada da Dr. Johnson Nebechi, Comrade...
Kalli Bidiyo Yanda wannan matar ke aikin da ake biyanta Naira Dubu 40 duk bayan awa daya

Kalli Bidiyo Yanda wannan matar ke aikin da ake biyanta Naira Dubu 40 duk bayan awa daya

Duk Labarai
Wannan wata mata ce da ta ke a kasar Amurka inda take aiki ana biyanta Naira Dubu 40 duk awa daya. https://www.youtube.com/watch?v=9HFjRK5j9mo Tace tana aiki ne a babban shagon sayayya na Amazon inda take aikin dare. Da yawa dai sun bayyana sha'awar aikin nata. Saidai wasu na ganin tsadar rayuwa da ake fama dashi a Amurka zai iya lakume kudaden da take samu.
Mutane 10 sun mùtù da dama sun jikkata a mummunan hadarin mota da ya faru a jihar Jigawa

Mutane 10 sun mùtù da dama sun jikkata a mummunan hadarin mota da ya faru a jihar Jigawa

Duk Labarai
Mutane 10 sun mutu da dama sun jikkata a wani mummunan hadarin mota da ya faru a jihar Jigawa. Lamarin ya farune a karamar hukumar Taura dake jihar. Wani Shaidar gani da ido ya gayawa manema labarai cewa hadarin ya farune a kauyen 'Yanfari dake kan hanyar Kano zuwa Hadejia a karamar hukumar Taura. Yace motar bas ce ta daki wata Tirela dake a gefen titi inda motar ta wuntsula mutane 10 suka mutu nan take. Kakakin 'yansandan jihar, DSP Lawan Shiisu ya tabbatar da faruwar lamarin. Yace lamarin ya farune ranar November 12, 2024 kuma suna samun labari jami'an su suka garzaya wajan inda yace sun tarar direban motar da mutane 9 sun mutu. Yace akwai mutum da ya da bai mutu ba a yanzu ana duba lafiyarsa. Yace suna kan bincike dan gano ko akwai laifin wani a hadarin da ya faru.
NNPC Ta Sanar Da Kammala Biyan Bashin Dala Bilyan 2.4, Tare Da Albishirin Samar Da Manyan Tashoshin CNG 12 A Shekara Mai Zuwa

NNPC Ta Sanar Da Kammala Biyan Bashin Dala Bilyan 2.4, Tare Da Albishirin Samar Da Manyan Tashoshin CNG 12 A Shekara Mai Zuwa

Duk Labarai
Shugaban rukunin Kamfanin Mai Na NNPC, Mele Kyari ne ya bayyana nasarar kammala biyan bashin da ake bin kamfanin da ga kamfanonin mai na kasashen ƙetare inda ya ce a yanzu, babu mai bin kamfanin bashin sisin kwabo.Kyari ya ce, wannan babban nasara ce da aka cimma biyo bayan cire tallafin mai a Gwamnatin Shugaba Tinubu. “Mun rika karkatar da kudadenmu da dukiyoyinmu don tabbatar da komai na tafiya daidai a bangaren mai na PMS mai wuyar sha'ani, abinda ya rika janye hankalin NNPC daga biyan basussuka" Mele ya ci gaba da cewa“ Sai dai yanzu wannan matsala ta kau, za ku ga cewa ba mu da wani bashin da ake bin mu, kuma don mu tabbatar da dorewar hakan, ya zama wajibi a kawar da duk wata matsala don masana'antar ta iya samar da makamashi mai dorewa da arha da ake buƙata a ƙasar nan." Sh...