
Idan da gaskene fahimtar da dan Sheikh Nura Khalid me suna Ibrahim da ya bar Musulunci yawa Hadisin da yasashi ya bar Musulunci, to ya kamata ya ja hankalin Mahaifinsa shima ya zama Kirista.
Amma idan fahimtarsa kuskurece akan Hadisin da yasa yayi ridda to muna fatan Sheikh Nura Khalid ya fahimtar dashi ya dawo dashi kan hanya.
Sannan babu Adalci a rika cewa jarrabawa ce akan Nura Khalid a rika hadashi da Jarabawar ridda da dan Sheikh Jafar Mahmud Adam Yayi
Sheikh Jafar baya goyon bayan Kiristoci sannan Tauhidi yake karantarwa sannan idan aka duba sauran ‘ya’yansa za’a ga yayi kokari wajan Tarbiyya dan haka riddar da dansa yayi Jarabawacw irin ta Annabi Nuhu(AS)
Amma shi Sheikh Nura Khalid Digital Imam nashi ba kaddara bane saboda yana goyon bayan Kiristoci ne.
Amma duk da haka ba Murna muke da fitar dan Nura Khalid zuwa Kiristanci ba, muna fatan Allah ya dawo dashi kan hanya
Inji Sheikh Musa Asadussunnah