Thursday, April 9
Shadow
Sanatoci sun ce in rokeka a sake duba janye musu jami’an tsaron ‘yansanda da aka yi, dan basu iya komawa garuruwansu haka ba jami’an tsaro>>Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu

Sanatoci sun ce in rokeka a sake duba janye musu jami’an tsaron ‘yansanda da aka yi, dan basu iya komawa garuruwansu haka ba jami’an tsaro>>Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu

Duk Labarai
Sanata Godswill Akpabio ya gayawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cewa sanatoci sun ce ya rokeshi ya sake duba janye musu jami'an tsaron da yayi. Sanata Akpabio ya gayawa shugaba Tinubu hakanne a yayin da shugaban ya je gabatar da kasafin kudin shekarar 2026a zauren majalisar. A baya dai shugaba Tinubu ya bayar da umarnin janyewa duk wani babba a kasarnan jami'an tsaron 'yansanda. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2002026911514366315?t=OqiCx2PMjD8NZBToUV1Umw&s=19
Sojojin Najeriya 11 da kasar Burkina Faso ta saki sun isa kasar Ghana

Sojojin Najeriya 11 da kasar Burkina Faso ta saki sun isa kasar Ghana

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, sojojin Najeriya guda 11 da kasar Burkina Faso ta saki tare da jirginsu C-130 sun isa kasar Ghana Rahoton yace sun samu tarba me kyau a kasar wanda hakan ke kara tabbatar da kyakkyawar alakar dake tsakanin Najeriya da kasar Ghana. Hakanan kuma a ranar Asabar ne zasu ci gaba da tafiyarsu zuwa kasar Portugal wadda dama can suka nufa suka makale a kasar Burkina Faso.
Man Fetur din Najeriya yayi kwantai a kasuwar Duniya

Man Fetur din Najeriya yayi kwantai a kasuwar Duniya

Duk Labarai
Rahotanni sun ce ganga kusan miliyan 20 na danyen man fetur din Najeriya da ake son sayarwa a tsakanin watannin Disamba zuwa January har yanzu yana nan ba'a sayar dashi ba. Kafar Reuters tace itama kasar Angola danyen man nata nacan Jibge an kasa sayar dashi. Rahoton yace kasashen biyu na ta kokarin ganin sun samu masu sayen danyen man fetur din nasu amma abu ya faskara. Rahotanni sun ce kasar China wadda tana daya daga cikin manyan masu sayen danyen man na kasashen Afrika ta fara komawa sayen man daga kasashen Larabawa saboda yafi saukin farashi da kuma saukin sufuri.
Da Duminsa: Rahotanni na cewa sojan da ya shirya jhuyin mulki a kasar Benin Republic ya samu tserewa zuwa kasar Nijar, inda aka bashi mafakar siyasa acan

Da Duminsa: Rahotanni na cewa sojan da ya shirya jhuyin mulki a kasar Benin Republic ya samu tserewa zuwa kasar Nijar, inda aka bashi mafakar siyasa acan

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, sojan da ya jagoranci juyin mulkin da bai yi nasara ba a kasar Benin Republic, Pascal Tigri yanzu haka yana zaune a kasar Nijar. Rahoton yace Pascal Tigri ya samu mafakar siyasa a kasar ta Nijar inda yanzu haka yake zaune a wani gidan gwamnati dake kusa da fadar shugaban kasar Nijar. Rahoton yace yanzu haka ana zargin kasar ta Nijar da hannu ko da ba kai tsaye bane a yunkurin juyin Mulkin. Pascal Tigri da farko ya tsallaka zuwa kasar Togo ne inda daga nan ya hau jirgi zuwa Burkina Faso. Daga baya kuma ya sake hawa jirgi zuwa kasar Nijar. Najeriya dai ta taimakawa kasar ta Benin Republic aka murkushe yunkurin juyin mulkin.
Mun Gama da ‘Yan Adawa: Yanzu sanatoci 5 ne kadai suka rage a jam’iyyar Adawa a majalisar Dattijai, suma se rokona suke in musu jagora zuwa gurin shugaban kasa su koma APC>>Inji Sanata Godswill Akpabio

Mun Gama da ‘Yan Adawa: Yanzu sanatoci 5 ne kadai suka rage a jam’iyyar Adawa a majalisar Dattijai, suma se rokona suke in musu jagora zuwa gurin shugaban kasa su koma APC>>Inji Sanata Godswill Akpabio

Duk Labarai
Sanata Godswill Akpabio ya bayyana cewa, a lokacin da ya zama kakakin majalisar Dattijai, akwai sanatoci kusan 50 a jam'iyyun adawa. Yace amma yanzu wanda ke jam'iyyar adawa basu wuce 4 zuwa 5 ba. Yace suma sai rokonsa suke ya kaisu wajan shugaban kasa su koma APC. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/2001970822454591647?t=WxAMejfKUrJ0YdoZOAuxJg&s=19