Kalli Yanda aka bi Duk Zamfara aka lalata duk wata fasta ta shugaba Tinubu, Jam’iyyar APC tace abin ya isheta haka
Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa wasu tsagera sun bi fastocin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun lalatasu a fadin jihar.
Sakataren yada labarai na jihar, Malam Yusuf Idris ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai.
Yace wannan cin fuskane wanda ba zasu yadda dashi ba inda yayi kira ga jami'an tsaro su dauki mataki kan lamarin.








