Monday, April 20
Shadow
Farashin Dala a kasuwar Chanji ta yau

Farashin Dala a kasuwar Chanji ta yau

Duk Labarai
Rahotanni daga kasuwar chanji ta yau na cewa farasin dala na akan Naira N1,450.25 kan kowace dala a kasuwar Gwamnati kenan. A kasuwar Bayan fage kuwa farashin yana kan tsakanin Naira 1,455 zuwa Naira 1,460 akan kowace dala. Masu sharhi a kasuwar dai sun bayyana cewa farashin ya dan daidaita baya yawan hawa da tashi.
A canjamin waje, Nifa ba zan iya zama a gidan Gyaran Hali na Sokoto ba>>Nnamdy Khanu ya koka

A canjamin waje, Nifa ba zan iya zama a gidan Gyaran Hali na Sokoto ba>>Nnamdy Khanu ya koka

Duk Labarai
Shugaban haramtacciyar kungiyar IPOB dake tsare a gidan yarin jihar Sokoto bayan yanke masa hukuncin daurin rai da rai, Nnamdy Khanu ya bayyana cewa, ba zai iya zama a gidan yarin na jihar Sokoto ba. Kanu ta hannun kaninsa, Prince Emmanuel Kanu, ya bukaci da kotun tarayya dake Abuja ta canja masa gidan yari. Yace dalili kuwa shine zamansa a gidan yarin sokoto ba zai bashi damar daukaka kara da yake son yi ba. Saidai me shari'a a kotun yace kanin na Nnamdi Kanu bashi da hurumin da zai iya shigar da wannan korafi, lauyane kawai ke da wannan hurumin. Sannan Alkalin yace game da maganar daukaka kara ba lallai sai Nnamdi Kanu yayi da kansa ba, wakilansa, watau Lauyoyi zasu iyayi.
Matashin da yace Sanata Ned Nwoko ya bashi kudi ya sashi ya Shyèkyè matarshi ya fito yace karya yake

Matashin da yace Sanata Ned Nwoko ya bashi kudi ya sashi ya Shyèkyè matarshi ya fito yace karya yake

Duk Labarai
Wani matashi da yayi Bidiyo yace sanata Ned Nwoko ya bashi udi yace ya kàshè matarsa, Regina Daniels ya fito yace karya yake. Matashin yace shi dama an sanshi da karya a shafin Tiktok. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1996715273051840622?t=QNB7vM7DII26U9q5z6R9kw&s=19 A Bidiyon farko da ya saki Wanda hutudole ya kawo muku jiya, Matashin yace Sanata Ned Nwoko ya basu Naira Miliyan 5 wai su kàshè matarsa Regina Daniels Bidiyon ya watsu sosai a kafafen sada zumunta.
Rabin Abuja Gidajen Inyamurai ne>>Inji Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima

Rabin Abuja Gidajen Inyamurai ne>>Inji Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima

Duk Labarai
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bayyana cewa, rabin Abuja Inyamurai ne suka mallaketa Hakanan rabin Legas ma kusan sune. Yace Inyamurai na da matukar muhummanci wajan ci gaban Najeriya. Yace duk inda kaje a fadin Najeriya baka ga Bahaushe ko Inyamuri ba to kada ka zauna. Ya bayyana hakane a wajan taron tattalin arziki da aka yi a jihar Imo. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1996621657499484606?t=Uuo7GNHTuS7X0DI9gpLS4g&s=19
Kalli Bidiyon: Matar Sabon Ministan tsaro, Christopher na shan Yabo kan yanda ta durkusa har kasa ta gaishe da shugaba Tinubu

Kalli Bidiyon: Matar Sabon Ministan tsaro, Christopher na shan Yabo kan yanda ta durkusa har kasa ta gaishe da shugaba Tinubu

Duk Labarai
Matar Ministan tsaro, Janar Christopher Musa ta sha yabo sosai kan yanda ta durkusa har kasa ta gaishe da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Lamarin ya farune a yayin da aka rantsar da Janar Christopher Musa a matsayin sabon Ministan tsaron a fadar shugaban kasa https://twitter.com/OzorNdiOzor/status/1996656303843037526?t=F85XFoOsAn5FWBfn9_Y0Aw&s=19
Bai kamata ace an nada Tsohon Shugaban INEC da ya sauka mukamin Jadaka ba, ni dai da nine shugaban kasa ba zan yi haka ba>>Inji Atiku Abubakar

Bai kamata ace an nada Tsohon Shugaban INEC da ya sauka mukamin Jadaka ba, ni dai da nine shugaban kasa ba zan yi haka ba>>Inji Atiku Abubakar

Duk Labarai
Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa bai kamata shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya nada tsohon shugaban INEC jakada ba Yace hakan zai sa wasu su yi zargin cewa watakila ya taimakawa Tinubun da magudin zabene shine yake saka masa da mukamin Jakada Yace shi dai da shine shugaban kasa ba zai aikata hakan ba. Farfesa Mahmoud Yakubu tsohon shugaban hukumar zabe me zaman kanta INEC na daga cikin sunayen da shugaba Tinubu yake son baiwa mukamin jakadanci.
Kwanannan cikin gaggawa zaku ga sakamako me kyau>>Sabon Ministan tsaro, Janar Christopher Musa ya bayar da tabbaci

Kwanannan cikin gaggawa zaku ga sakamako me kyau>>Sabon Ministan tsaro, Janar Christopher Musa ya bayar da tabbaci

Duk Labarai
Sabon Ministan tsaro Janar Christopher Musa ya bayar da tabbacin cewa kwanannan cikin gaggawa za'a ga sakamako me kyau. Ya bayyana hakane a ganawa da manema labarai a Abuja bayan rantsar dashi a matsayin Ministan tsaro. Yace zai hada kai da dukkan wadanda suka kamata dan tabbatar da an samar da tsaro a Najeriya. https://twitter.com/NigAffairs/status/1996641245184348248?t=qaH47c5nZFVeSavT_o7s9w&s=19
Majalisar Dattijai zata yi dokar saka ido da kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu

Majalisar Dattijai zata yi dokar saka ido da kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu

Duk Labarai
Majalisar Dattijai na shirin yin sabuwar doka dan kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu. Dayake magana akan muhimmancin wannan doka, Sanata Adams Oshiomhole ya bayyana cewa, an taba sace masa kudi a asusun bankinsa kuma inda aka tura kudaden Opay ne da Moniepoint. Yace kuma basu da rassa a zahiri da mutum zai ce ya shigar da korafi. dan haka akwai bukatar a yi dokar da zata saka ido a ayyukan da suke. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1996645682640265295?t=qvwu4FHmYIHsrWjka2UMqQ&s=19 Ita kuma a nata bangaren, Sanata Natasha Akpoti ta bayyana cewa wai idan aka yi wannan doka zata taimakawa matasan Najeriya dake samun kudi ta yanar gizo su rika samu daidai da takwarorinsu na kasashen waje. https://twitter.com/ChuksEricE/status/19...