Wednesday, February 25
Shadow
Kalli Bidiyo: Sa in Sar da Sanata Barau Jibrin yayi inda yake cewa baya tsoron Donald Trump, Abin Kunyane ya jawowa yankin Arewa>>Inji Wannan matashin

Kalli Bidiyo: Sa in Sar da Sanata Barau Jibrin yayi inda yake cewa baya tsoron Donald Trump, Abin Kunyane ya jawowa yankin Arewa>>Inji Wannan matashin

Duk Labarai
Wannan matashin da Bidiyonsa ke kasa yace abin kunyane Sanata Barau Jibrin ya jawowa Yankin Arewa tashin da yayi suka yi sa'insa da kakakin majalisa, Sanata Godswill Akpabio akan harin da Shugaban kasar Amurka, Donald Trump yace zai kawowa Najeriya. Shi dai sanata Barau yace baya jin tsoron Shugaban Amurka, Donald Trump sannan ya bayyanashi da matsoraci inda yayi kira ga kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio shima ya daina jin tsoron Trump. Saidai Matashin yace sam abinda sanata Barau Jibrin Maliya yayi bai kyauta ba. Yace a baya Sanatan bai taba tashi ya nuna damuwa ba kan matsalar tsaron Arewa sai yanzu dan Trump yace zai kawo Khari? https://www.tiktok.com/@01___abdull/video/7569012826832981269?_t=ZS-918zMMoLdyq&_r=1
Kalli Bidiyo: Ba hakkin Miji bane ya kula da Rashin Lafiyar matarsa, Hakkin Iyayenta ne>>Inji Malam Dr. Ibrahim Jalo Jalingo

Kalli Bidiyo: Ba hakkin Miji bane ya kula da Rashin Lafiyar matarsa, Hakkin Iyayenta ne>>Inji Malam Dr. Ibrahim Jalo Jalingo

Duk Labarai
Malamin Addinin islama, Dr. Ibrahim Jalo Jalingo ya bayyana cewa ba hakkin miji bane ya kula da rashin lafiyar matarsa. Yace hakkin iyayenta ne amma idan miji yayi, ya kyautata. Malam ya bayyana hakane bayan da aka masa tambaya kan rikicin dake faruwa da kuma sa insa da ake akan maganar. https://www.tiktok.com/@ameenwarkal/video/7568833251888942354?_t=ZS-918svzZWwPx&_r=1
Ko Kadan Bana Jin tsoron Shugaban Amurka Donald kuma nasan Maqaryacine saboda yawa kasarmu karya>>Inji Sanata Barau Jibrin

Ko Kadan Bana Jin tsoron Shugaban Amurka Donald kuma nasan Maqaryacine saboda yawa kasarmu karya>>Inji Sanata Barau Jibrin

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Sanata Barau Jibrin Maliya ya bayyana cewa ko kadan baya jin tsoron shugaban kasar Amurka, Donald Trump inda yace Shi dan Najeriya ne kasa me cin gashin kanta, kuma dan Majalisa, kuma mataimakin kakakin majalisar Dattijai dan haka sai ya fadi ra'ayinsa. Ya bayyana cewa, Trump yawa Najeriya karya dan haka ya kamata a gaya masa bai yi daidai ba. Sannan ya gayawa Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio cewa shima ya daina jin tsoron Trump ya fito ya fadi abinda ke zuciya...
Satar Arziki ne zai kawo Trump Najeriya ba taimakon Kiristoci ba>>Inji Kungiyar Kare Muradun Yarbawa, Afenifere

Satar Arziki ne zai kawo Trump Najeriya ba taimakon Kiristoci ba>>Inji Kungiyar Kare Muradun Yarbawa, Afenifere

Duk Labarai
Kungiyar Kare muradin yarbawa ta Afenifere ta bayyana cewa, shugaban kasar Amurka, Donald Trump zai shigo Najeriya ne da niyar satar arzikin kasa amma ba maganar tseratar da Kiristoci ba. Kungiyar ta bakin sakataren yada labarinta, Mr. Jare Ajayi tace hujjar da Trump ya kawo ta banza ce kawai yana neman hanyar shigowa Najeriya ne. Yace Trump na son amfani da wannan damar ne wajan tilasta Najeriya sayen abubuwa daga Amurka musamma makamai saboda baya jin dadin huldar da Najeriya ke yi da kasar China. Yace sannan Amurkar ta ji haushin kalaman da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima yayi a taron majalisar Dinkin Duniya inda ya goyi bayan kafa kasar Falasdiynawa. Kungiyar ta yi kira ga 'yan Najeriya dama shuwagabannin da su kaucewa yin kalaman da zasu kara zhugha Amurka tace ...
Da Duminsa: A karin Farko Musulmi ya zama magajin garin New York City, na kasar Amurka

Da Duminsa: A karin Farko Musulmi ya zama magajin garin New York City, na kasar Amurka

Duk Labarai
Zohran Mamdani wanda musulmi ne ya ci zaben magajin garin New York City a kasar Amurka. Wannan shine karin farko da hakan ta faru a tarihin Birnin Na New York, hakanan Zohran Mamdani dan Asalin kasar Uganda ne, daga baya ya je kasar Amirka ya zama dan kasa. Zohran Mamdani ya kayar da tsohon gwamnan jihar New York Andrew Cuomo wanda Shugaban kasar, Donald Trump da Attajirin Duniya Elon Musk suka goyi baya. A baya dai, Donald Trump yace idan Zohran Mamdani ya ci zaben magajin garin New York, zai dakatar da kudaden da gwamnatin tarayya ke aikawa birnin.
Baku isa ku hanamu kare kiristoci a Najeriya ba>>Sanatan Amurka ya mayarwa da China Martani

Baku isa ku hanamu kare kiristoci a Najeriya ba>>Sanatan Amurka ya mayarwa da China Martani

Duk Labarai
Sanatan kasar Amirka, Riley Moore ya mayarwa da kasar China martani bayan da ta gargadi America da cewa kada ta yi katsalandan akan harkar tsaron cikin gida Najeriya Sanatan yace shugaban kasarsu Trump akan Daidai yake kuma babu wanda zai hanashi kaiwa Kiristoci dauki a Najeriya Yace Ba China ce zata koya musu hulda da kasashen wajeba. https://twitter.com/RepRileyMoore/status/1985750168281698655?t=a9vfqCSiDNYmEKnvsuI-Hg&s=19
Ba addini ne kawai ke haifar da rikicin Najeriya ba – EU

Ba addini ne kawai ke haifar da rikicin Najeriya ba – EU

Duk Labarai
Ƙungiyar Tarayyar Turai ta EU ta ce ta fahimci cewa ba addini ne kaɗai ke haifar da rikice-rikice a Najeriya ba. Cikin wata sanarwa kakain ƙungiyar da Anouar El Anouni ya fitar ya ce ƙungiyar EU na jajanta wa imjutanen da rikicin ya rutsa da su kudanci da arewa maso gabashin ƙasar. Matakin na ƙungiyar EU na zuwa ne bayan da shugaban Amurka, Donald Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya, kan abin da ya kira kisan Kiristoci a ƙasar. Sai dai EU ta ce akwai abubuwa da dama da ke haifar da rikicin ba addini kaɗai ba. “Mun fahimci cewa akwai abubuwa masu yawa da ke haifar da rikici a Najeriya, addini guda ne daga cikinsu, amma ba shi kaɗai ba,'' in ji Mista El Anouni.