Friday, February 27
Shadow
Tabbas Ministan Kudi bashi da lafiya, kuma ta dan yi tsanani, amma ba shanyewar rabin jiki bace>>Fadar Shugaban kasa

Tabbas Ministan Kudi bashi da lafiya, kuma ta dan yi tsanani, amma ba shanyewar rabin jiki bace>>Fadar Shugaban kasa

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa, ta tabbatar da cewa, ministan Kudi, Wale Edun Bashi da lafiya Wata majiya daga fadar ta tabbatar wa da gidan jaridar Punchng hakan inda tace rashin lafiyar ta matsa masa. Saidai tace ba Shanyewar rabin jiki bane sannan ba'a fitar dashi zuwa kasar waje ba, sannan shugaban kasa Bola Tinubu bai fara neman wanda zai maye gurbinsa ba. Rahotanni sun ce Likitocin Najeriya ne ke kula da Ministan amma idan lamarin yayi kamari za'a iya fita dashi kasar waje.
Kalli Bidiyo: Matashi me suna Abdullahi, wada yace shi dan Izala ne, ya bar Musulunci inda ya koma Kirista

Kalli Bidiyo: Matashi me suna Abdullahi, wada yace shi dan Izala ne, ya bar Musulunci inda ya koma Kirista

Duk Labarai
Wani matashi daga jihar Katsina wanda yace ya fito ne daga garin Radda na jihar katsina kuma da uwane a wajan gwamnan Katsina watau Dikko Raddah ya koma Kirista. Matashin wanda yace sunansa Abdullahi yace ya koma Kirista ne a Makaranta bayan da ya fara karanta Baibul ya kuma fahimceshi. Matashin yace da ya gayawa mahaifiyarsa ta dauki abin da wasa amma daga baya da aka ga da gaske yake, an kamashi an daure tsawon watanni indaa yace amma duk da haka bai koma musulmi ba. https://www.tiktok.com/@chizo_1_germany/video/7559944553420295446?_t=ZS-90VjSzhe8RM&_r=1
Kalli Bidiyon: Shima Dan Tiktok, Auwal ya musuluntar da Wadda suke wasan Barkwanci tare, Christy ta koma Fatima

Kalli Bidiyon: Shima Dan Tiktok, Auwal ya musuluntar da Wadda suke wasan Barkwanci tare, Christy ta koma Fatima

Duk Labarai
Dan Tiktok me wasan Barkwanci, Auwal ya musuluntar da wadda suke wasan Barkwanci tare me suna Christy ta koma musulma inda ta zabi sunan Fatima. A Bidiyon da ya wallafa, an ganshi inda suka je masallaci tare da ita. Sannan itama ta tabbatar da cewa, da gaskene ta karbi Addinin Musulunci. https://www.tiktok.com/@auwal.44/video/7559721807893368082?_t=ZS-90ViIEMEJ0L&_r=1
Kalli Bidiyon: Na kasa Fahimtar me nene Shugaban Kungiyar Izala, Bala Lau yace suna tare da Malam Lawal Triumph akai, Kalaman batancin da yayiwa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ko mene?>>Sheikh Farfesa Ibrahim Maqari ya bayyana

Kalli Bidiyon: Na kasa Fahimtar me nene Shugaban Kungiyar Izala, Bala Lau yace suna tare da Malam Lawal Triumph akai, Kalaman batancin da yayiwa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ko mene?>>Sheikh Farfesa Ibrahim Maqari ya bayyana

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Farfesa Ibrahim Maqari ya bayyana cewa, yana mamakin kalaman da Shugaban Izala, Sheikh Bala Lau yayi da yace suna tare da Malam Lawal Triumph. Malam Maqari ya bayyana cewa, abinda ya bashi mamaki shine shin wai akan me Izala take tare da Malam Lawal Triumph akan kalaman batancin da yawa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ko mene?. Malam ya bayyana hakane a wani Bidiyonsa da ya dauki hankula sosai inda yake cewa Ibn Taimiyya yace girmama Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) da kambamashi shine ke nuna tsayuwar Addini. https://www.tiktok.com/@hassan.a.hassan.2/video/7559949237786512652?_t=ZS-90VfCQzDGTY&_r=1
Rahotanni sunce Shugaba Tinubu ya fara neman wanda zai nada a matsayin sabon Ministan kudi, bayan da Ministan Kudi Wale Edun ya samu rashin lafiyar Shanyewar rabin jiki

Rahotanni sunce Shugaba Tinubu ya fara neman wanda zai nada a matsayin sabon Ministan kudi, bayan da Ministan Kudi Wale Edun ya samu rashin lafiyar Shanyewar rabin jiki

Duk Labarai
Rahotanni sun ce tuni shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya fara neman wanda zai maye ministan Kudi, Wale Edun dashi. Ministan Kudi, Wale Edun ya kwanta rashin lafiya bagtatan inda rahotanni suka ce shanyewar rabin jiki ce ta kamashi. Rahotannin sun ce an garzaya dashi zuwa kasar waje. Hakanan rahotannin sun ce ko da ya warke da wuya ya iya komawa bakin aikinsa. Wannan ne yasa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya fara meman wanda zai maye gurbinsa dashi. Rahotanni sun ce Shugaba Tinubu ya baiwa Gwamnan Babban bankin Najeriya, CBN umarnin maye gurbin Ministan kudin a wai taro da za'a yi a kasashen waje.
Ji yanda matar aure a Arewa ta yi yaji saboda Mijinta yana bata Dubu dari a wata a matsayin kudin Cefane,tace sun yi kadan

Ji yanda matar aure a Arewa ta yi yaji saboda Mijinta yana bata Dubu dari a wata a matsayin kudin Cefane,tace sun yi kadan

Duk Labarai
Wata matar aure a Arewa ta yi yaji saboda tace mijinta yana cutar da ita saboda 'ya'yansu 2 amma sai ya rika bata kudin cefanane Tace yana ajiye kayan abinci kamar buhun shinkafa da man girki, amma sai ya bata Naira 100,000 wanda baya isanta yon cefane. Akan hakane suka yi fada ta tafi gidansu. https://twitter.com/_hafsat_paki/status/1977371222385029269?t=NsYHM3ZBZ_rvBAvum_wEbQ&s=19
Wannan wani Gawurtaccen Me Shatar mutanene dan neman kudin fansa wanda yana cikin wadanda shugaba Tinubu yawa afuwa

Wannan wani Gawurtaccen Me Shatar mutanene dan neman kudin fansa wanda yana cikin wadanda shugaba Tinubu yawa afuwa

Duk Labarai
Kelvin Oniarah Ezigbe dan shekaru 44 na daga cikin mutanen da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yawa afuwa. Shugaban wasu gungun 'yan fashine dake garkuwa da mutane An zargeshi da hannu a kisan Sojoji da 'yansanda da dama. An yanke masa hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari saidai saboda nuna nadama da yayi, an rage shekarun zuwa 13.
Da Duminsa: Cutar Shanyewar Rabin jiki ta kama Ministan kudin Najeriya an garzaya dashi asibitin kasar waje

Da Duminsa: Cutar Shanyewar Rabin jiki ta kama Ministan kudin Najeriya an garzaya dashi asibitin kasar waje

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, cutar Shanyewar rabin jiki ta kama Ministan Kudi, Wale Edun inda aka garzaya dashi zuwa asibitin kasar waje Sahara reporters ta bayyana cewa, lamarin yayi tsanani anma yana samun kulawa ta musamman a asibitin da aka kaishi. Rahotan yace ministan yana aiki da yawa ba tare da hutu ko cin abinci yanda ya kamata ba wanda ake ganin hakan ya taimaka sosai wajan rashin lafiyar tasa. Rahoton yace Gwamnan babban bankin Najeriya CBN, Cordoso ne aka wakilta ya maye gurbin ministan zuwa wani babban taron kudi da za'a yi a kasashen waje. Rahoton yace ko da ministan ya warke da wuya ya koma bakin aikinsa inda rahotanni suka ce tuni shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya fara neman wanda zai nada a matsayin sabon Ministan kudin. rahoton yace fadar shugaban kasa t...