Monday, May 19
Shadow
Tinubu ya dawo da zaman lafiya a Arewa-maso-Yamma, inji Gwamnan Kaduna, Uba Sani

Tinubu ya dawo da zaman lafiya a Arewa-maso-Yamma, inji Gwamnan Kaduna, Uba Sani

Duk Labarai
Tinubu ya dawo da zaman lafiya a Arewa-maso-Yamma, inji Uba Sani. Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya daidaita harkar tsaro a yankin Arewa maso Yamma tare da farfado da harkokin noma da 'yan ta'adda suka durkusar da su a baya. Da yake jawabi a taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC na Arewa maso Yamma da aka gudanar a Kaduna ranar Asabar, Sani ya ce yankin da a da ke zama cibiyar ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma ayyukan ‘yan bindiga, yanzu yana samun sauyi mai ma’ana. “Tun kafin Shugaba Tinubu ya hau mulki a shekarar 2023, yankin Arewa maso Yamma ne cibiyar ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran laifukan tashin hankali,” in ji shi. “Ba za ka iya yin tafiya daga wuri zuwa wani wuri ba. Manoma ba za su iya zuwa gonakinsu ba. Rayuwa ta kasance...
Akwai fargabar dabbobi za su yi tsada lokacin babban sallah a Najeriya

Akwai fargabar dabbobi za su yi tsada lokacin babban sallah a Najeriya

Duk Labarai
Haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu fataucin dabbobi da kayan abinci a Najeriya, ta ce akwai fargabar dabbobi za su iya yin tsada a lokacin babbar sallah. Sun ce hakan zai iya faruwa ne saboda takunkumin da gwamnatin Nijar ta saka na haramta fitar da dabbobi zuwa ƙasashen waje. Ƴan kasuwar sun roki hukumomin Nijar su kalli maslahar al’umma su cire haramcin. Shugaban ƙungiyar, Dakta Muhammad Tahir ya shaida wa BBC cewa za a samu koma-baya a harkar sayar da dabbobi. "Idan gwamnatin Nijar tana ganin matakin da ta ɗauka shi ne zai kawo saukin abubuwa, to gaskiya akwai matsala, saboda ƴan Nijar da ke hada-hadar dabbobin idan ba su samu mai saye ba babban koma-baya ne," in ji shi. Ya ce akwai shanu da raguna sama da 50,000 waɗanda aka saya daga Chadi, inda yanzu haka suke maƙale a iyakar Cha...
Gwamnatin Borno ta haramta sare itatuwa ba bisa ka’ida ba

Gwamnatin Borno ta haramta sare itatuwa ba bisa ka’ida ba

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Borno ta amince da kudurin haramta sare itatuwa ba bisa ka'ida ba a faɗin jihar. Gwamna Babagana Umara Zulum ne ya sanar da haka ranar Juma'a, inda ya ce an ɗauki matakin ne domin kare muhalli da inganta lafiyar al'umma. Haka kuma, gwamnan ya amince da kudurin tsaftace muhalli wanda za a riƙa yin shara a a kowace Asabar ɗin farkon wata a faɗin jihar. "A don haka, duk wani mutum da aka samu yana sare itatuwa ba bisa ka'ida ba, za a ci tararsa naira 250,000 ko kuma ɗaurin shekara uku a gidan yari. Idan ya sake aikata laifin, hukuncinsa shi ne ɗaurin shekara biyar ko tarar naira 500,000 ko kuma a zartas masa da duka hukuncin," in ji gwamna Zulum. Gwamnan ya ce waɗanda aka samu ba sa tsaftace muhallinsu za a ci su tarar da ta kai naira 100,000 saboda saɓa wa umarnin...
Tinubu zan mara wa baya a zaɓen 2027 – Wike

Tinubu zan mara wa baya a zaɓen 2027 – Wike

Duk Labarai
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce ba zai yi takarar shugaban ƙasa a shekarar 2027 ba, sannan zai mara wa Tinubu baya. Wike ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da sashen Pidgin na BBC, inda ya ce har yanzu shi ɗan jam'iyyar PDP ne. "Ba zan sake yin takara ba. Ba zan yi takara da mutumin da nake yi wa aiki ba. Waye zai yi nasara idan ba shi ba?" kamar yadda Wike ya faɗa. Wike wanda ya kasance tsohon gwamnan jihar Rivers, ya yi takarar zaɓen fidda gwani na jam'iyyar PDP don zama ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen 2023, sai dai ya yi rashin nasara a hannun tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar. Ministan na Abuja ya kuma nuna ɓacin-ransa kan matakin jam'iyyar na kin ware tikitin takarar shugaban ƙasa wa yankin kudu, abin da ya janyo ta faɗa rikici...
Kudi na Kauye: Mutanen Kauyen Bauchi Dake kan hanyar zuwa Saudiyya sun dauki hankula bayan da suka dauki hotuna da farar Budurwa me aiki a cikin jirgin sama

Kudi na Kauye: Mutanen Kauyen Bauchi Dake kan hanyar zuwa Saudiyya sun dauki hankula bayan da suka dauki hotuna da farar Budurwa me aiki a cikin jirgin sama

Duk Labarai
Mutanen Bauchi dake kan hanyar zuwa Kasar Saudiyya sun dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta bayan da aka gansu suna daukar hotuna da farar budurwa me aikin cikin jirgi. Da yawa sun bayyana sha'awar lamarin inda aka rika cewa kudi na Kauye https://twitter.com/Sadeeq_Malo/status/1923781115208233070?t=0VK5P3ufXddZ4Ts4xyU_Jg&s=19 Hotunan sun dauki hankula sosai.
Jami’in ‘Civil Defence’ ya tsinci guzirin wata maniyyaciya a sansanin alhazai na Yola ya kuma mayar mata

Jami’in ‘Civil Defence’ ya tsinci guzirin wata maniyyaciya a sansanin alhazai na Yola ya kuma mayar mata

Duk Labarai
Jami'in 'Civil Defence' ya tsinci guzirin wata maniyyaciya a sansanin alhazai na Yola ya kuma mayar mata. Wani Jami’in hukumar tsaro ta 'Civil Defence' mai suna Abubakar Abdulƙadir Mayos, ya mayar da kuɗin guzirin wata maniyyaciya da ya tsinta, har Dalar Amurka $505 da Riyal 30 na Saudiyya a sansanin alhazai na birnin Yolan Jihar Adamawa ya kuma miƙa su ga mai su. Rahotanni sun baiyana cewa kuɗaɗen mallakar wata maniyyaciya, mai suna Maimuna Salihu Abdullahi, ƴar Jihar Taraba. Nan take, a cewar rahotanni ya mayar da kuɗin ga jami'an alhazai inda su kuma ba su yi wata-wata ba su ka miƙa mata kayanta a gaban jami’in hukumar NAHCON da daraktan tsare-tsare na hukumar alhazai ta Taraba da sauran jami’ai.
APC tace a kul EFCC kada ta sake ta binciki tsohon tsageran Naija Delta, Tampolo, duk da ganin Bidiyon sa yana wulakanta Naira

APC tace a kul EFCC kada ta sake ta binciki tsohon tsageran Naija Delta, Tampolo, duk da ganin Bidiyon sa yana wulakanta Naira

Duk Labarai
Sakataren jam'iyyar APC reshen kudu maso kudu, Dr Blessing Agbomhere ya aikawa shugaban hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC, Ola Olukoyede da wasika cewa Tampolo bai aikata komai ba. Wata majiya daga EFCC ce ta bayyanawa kafar jaridar Leadership da hakan. Sakataren APC din yace Tampolo bai aikata komai ba wanda ya sabawa Doka. Dr. Agbomhere wanda kuma lauyan Tampolo ne yace EFCC ta janye takardar gayyatar da tawa Tampolo. Duk wannan na faruwane bayan da aka ga Tampolo a wajan wani biki yana wulakanta Naira, abinda hukumar ta EFCC ta hukunta mutane da yawa a Najeriya saboda shi. Da yawa sun ce indai wannan doka ba ta son kai bace, ya kamata a gayyaci Tampolo, saidai da yawa na ganin hakan ba zai yiyu ba. Saidai Tuni EFCC ta aikewa da Tampolo takardar gayyata inda t...
Kalli Bidiyo: Sabuwar Motar Mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara ta Naira Miliyan 100 ta tayar da kura, motar da wutar Lantarki take amfani, watau ba’a zuba mata Fetur ko Gas

Kalli Bidiyo: Sabuwar Motar Mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara ta Naira Miliyan 100 ta tayar da kura, motar da wutar Lantarki take amfani, watau ba’a zuba mata Fetur ko Gas

Duk Labarai
Wannan Itace: Sabuwar motar Fitaccen Mawakin Siyasa A Nijeriya Alhaji Dauda Adamu Abdullahi (Kahutu Rarara). https://www.tiktok.com/@kahuturarara/video/7505486972647902519?_t=ZM-8wS1hWPvI2w&_r=1 Mai suna VinFast VF 8 wadda kamfanin VinFast na kasar Vietnam ke kerawa, Inda Yayu Matukar Ɗaukar Hankulan Mutane da Sabuwar Motar Ta Sa ta Miliyoyin Nairori. A binciken da hutudole yayi kudin motar ya kai naira Miliyan 86,240,000. Sannan motar da wutar Lantarki take amfani watau bata amfani da Gas ko Fetur. Wane Fata Zakuyi Mashi?
Kalli Bidiyon yanda sojojin Najeriya suka lakadawa ‘yansanda dukan kawo wuka suna kuka suna basu hakuri bayan da ‘yansandan suka daki wani soja

Kalli Bidiyon yanda sojojin Najeriya suka lakadawa ‘yansanda dukan kawo wuka suna kuka suna basu hakuri bayan da ‘yansandan suka daki wani soja

Duk Labarai
Wani Bidiyo ya bayyana a kafafen sada zumunta inda aka ga sojoji na dukan wasu 'yansanda hadda kwace musu Bindiga. An ga daya daga cikin 'yansandan na kuka. https://twitter.com/Akinjoshua2017/status/1923841553677636093?t=jPY-cIhPcnHBnrgvaT5hbw&s=19 Rahotanni dai yace 'yansandan sun kama wani soja ne akan cewa bai basu cin hanci ba inda suka lakada masa dukan tsiya.