Thursday, April 16
Shadow
Matashiya ‘yar Arewa na ta shan yabo bayan ganinta tana sana’ar Fenti

Matashiya ‘yar Arewa na ta shan yabo bayan ganinta tana sana’ar Fenti

Duk Labarai
Matashiya me sana'ar Fenti 'yar Arewa ta dauki hankula sosai a kafafen sadarwa. Da yawa sun jinjina mata ganin cewa ta dogara da kanta, bata tsaya sai wani ya bata ba. https://www.tiktok.com/@meerah4725/video/7627965053609839880?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7627965053609839880&source=h5_m&timestamp=1776164632&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7625183675001341712&share_link_id=7a7d516a-db0e-4f81-b69d-3aa64af11fa6&share_app_id=1233&ugbiz_name=MAIN&ug_btm=b2001...
Da Duminsa: Babbar kotun tarayya ta bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Da Duminsa: Babbar kotun tarayya ta bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Rahotanni daga Babbar kotun tarayya dake da zama a Kaduna sun bayyana cewa, Kotun ta bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Hakan na zuwane a yayin da yake fuskantar Tuhume-Tuhume 9 da gwamnatin tarayya take masa. A baya dai babbar kotun jihar Kaduna ta bayar da hakuri inda tace magabar belin malam Nasiru sai ranar 21 ga watan Aprilu zata yi hukunci akai.
Kalli Bidiyon: Saboda karamata, na taba tuka mota tsawon watanni 2 babu fetur a cikinta>>Inji Wannan faston

Kalli Bidiyon: Saboda karamata, na taba tuka mota tsawon watanni 2 babu fetur a cikinta>>Inji Wannan faston

Duk Labarai
Wani fasto ya dauki hankula sosai a kafafen aada zumunta bayan da yace ya taba tuka mota tsawon watanni 2 ba tare da fetur a cikin motar ba. Faston ya kuma ce diyarsa ta taba gaya masa cewa, babu gas din girki ya kare, yace kuma gashi bashi da kudi, shine kawai ya shafa jikin gas din sai da aka yi girki da gas din na tsawon watanni 3 ba tare da zuba masa gas ba. https://twitter.com/i/status/2043944470350016879
Da Duminsa: Ji Wani Tuggu da ake shiryawa dan hana Farfesa Isa Ali Pantami takarar Gwamna a jihar Gombe

Da Duminsa: Ji Wani Tuggu da ake shiryawa dan hana Farfesa Isa Ali Pantami takarar Gwamna a jihar Gombe

Duk Labarai
RIGIMA TA ƁARKE A APC A GOMBE, ZA A HANA PANTAMI TAKARAKA. Rahotanni sun nuna cewa Gwamnan jihar Gombe, Inuwa Yahaya, ya bukaci tsohon Ministan Sadarwa, Prof. Isa Ali Pantami, da ya janye burinsa na takarar gwamna tare da mara wa ɗan takarar da jam’iyyar APC za ta tsayar baya. An ce wannan ya faru ne a wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a daren yau a Gidan Gwamnatin jihar Gombe. Majiyoyi sun bayyana cewa Pantami bai ji daɗin wannan shawara ba, lamarin da ka iya haifar da sabani a cikin jam’iyyar. Me kuke ganin zai biyo baya a siyasar Gombe? Daga DDLHausa
Da Duminsa:Ji Hukuncin da kotu ta yanke kan bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai da ya baiwa mutane mamaki

Da Duminsa:Ji Hukuncin da kotu ta yanke kan bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai da ya baiwa mutane mamaki

Duk Labarai
kotu ta ɗage buƙatar bayar da belin tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai Zuwa Ranar 21 Ga Wannan Watan. Alƙalin da ke jagorantar shari’ar a Babbar Kotun Jiha a ƙarar ICPC da El-Rufa’i ya nemi afuwa bisa gazawar gabatar da hukunci kamar yadda aka tsara, yana mai danganta hakan da ƙarancin lokaci. Saboda haka, an ɗage sauraron buƙatar beli zuwa ranar Talata, 21 ga Afrilu, 2026.
Kalli Bidiyon: Duk da wajan Taron Rainbow yacewa jam’iyyar ADC ya fasa basu dakin taron da zasu yi babban taronsu saboda Wike ya hanasu, Jam’iyyar ta ADC tace babu gudu ba ja da baya sai sun yi taronsu a wajan saidai duk abinda zai faru ya faru

Kalli Bidiyon: Duk da wajan Taron Rainbow yacewa jam’iyyar ADC ya fasa basu dakin taron da zasu yi babban taronsu saboda Wike ya hanasu, Jam’iyyar ta ADC tace babu gudu ba ja da baya sai sun yi taronsu a wajan saidai duk abinda zai faru ya faru

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC tace zata gudanar da babban taronta a dakin taro na Rainbow dake Abuja duk da cewa dakin taron yace ya fasa basu wajan saboda an masa barazanar kwace masa lasisinsa. Saidai me magana da yawun jam'iyyar ta ADC, Bolaji Abdullahi yace ba gudu ba ja da baya sai sun gudanar da taronsu a wajan dan sun sakawa takardar yarjejeniya hannu. Tuni aka ga Bidiyon wajan taron sun fara bayyana a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/i/status/2043944090287411706
Kalli Bidiyon abin Kunya: Kakakin majalisar jihar Adamawa wanda dan APC ne ya je kauyensu wajan taron siyasa yace Najeriya, yana tsammanin za’a ce sai Tinubu, sai jama’a suka ce sai Atiku

Kalli Bidiyon abin Kunya: Kakakin majalisar jihar Adamawa wanda dan APC ne ya je kauyensu wajan taron siyasa yace Najeriya, yana tsammanin za’a ce sai Tinubu, sai jama’a suka ce sai Atiku

Duk Labarai
Kakakin majalisar jihar Adamawa ya je garinsu inda ya tara taron siyasa dan yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yakin neman zabe. Saidai a yayin da ya tashi zai yi bayani yace, Najeriya, sai aka ce masa sai Atiku a yayin da yake tsammanin ace masa sai Tinubu. https://twitter.com/i/status/2043965596111434080
Da Duminsa: Wajan taron Rainbow da muka shirya yin babban taron mu na kasa a yau, yace ya fasa bamu wajan saboda Gwamnati ta masa barazanar kwace lasisinsa idan ya bamu>>Inji Jam’iyyar ADC

Da Duminsa: Wajan taron Rainbow da muka shirya yin babban taron mu na kasa a yau, yace ya fasa bamu wajan saboda Gwamnati ta masa barazanar kwace lasisinsa idan ya bamu>>Inji Jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC ta bayyana cewa wajan taro na Rainbow data shirya yin taronta na kasa a yau, Talata ya sanar da ita cewa ya fasa bata wajan. Me magana da yawun ADC, Bolaji Abdullahi ne ya bayyana haka a wata sanarwa inda yace, Rainbow ya basu dalilin cewa, Hukumar kula da babban birnin tarayya, Abuja, FCTA ce ta musu barazanar cewa idan suka bayar da wajan za'a kwace lasisinsu. Saidai Bolaji Abdullahi yace sun riga sun sakawa takardar yarjejeniya da raibow hannu dan haka ba zasu fasa ba a wajan zasu yi taronsu.