Thursday, July 16
Shadow
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya gabatar da  fom dinsa na takara bayan ya cike ga jam’iyyar APC inda kuma ya bayyana Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya gabatar da fom dinsa na takara bayan ya cike ga jam’iyyar APC inda kuma ya bayyana Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya mayarwa da jam'iyyar APC fom din takarar shugaban kasa bayan ya kammala cikawa. Sannan ya bayyana Kashim Shettima a matsayin abokin takarar sa na zaben shekarar 2027. Me baiwa shugaban kasar shawara akan harkokin Siyasa, Ibrahim Masari ne ya wakilci shugaban kasar wajan mika wannan fom. https://twitter.com/i/status/2075624224241090932
Da Duminsa: Mansurah Isah tawa Rarara wankin babban Bargo tace ta bar Triple R kuma ya kiyayeta shi da yaransa in ba haka ba idan ta fara tone-tone ba za’a ji dadi ba

Da Duminsa: Mansurah Isah tawa Rarara wankin babban Bargo tace ta bar Triple R kuma ya kiyayeta shi da yaransa in ba haka ba idan ta fara tone-tone ba za’a ji dadi ba

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah Ta bayyana cewa, Ta bar tafiyar Triple R ta Rarara amma ta ji kananan maganganu suna biyowa baya. Ta yi gargadin cewa, idan aka ci gaba zata yi tone-tone. Sannan tace Yanda suka yi da Rarara shine yace mata ta zaba ko shi ko dan shugaban kasa, shine tace ta zabi dan Shugaban kasa. Saidai a kasan shafin Mansurah Isah Matar Rarara tace Mansurah me yasa ta kira sunanta dan ita bata ga abinda ya hadata da ita ba.
Wata Sabuwa Kalli Bidiyon: Mata 4 sun fitar da update din malamin jami’ar da akawa na jaki saboda neman matar aure

Wata Sabuwa Kalli Bidiyon: Mata 4 sun fitar da update din malamin jami’ar da akawa na jaki saboda neman matar aure

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wasu mata 4 sun fito suma sun bayyana cewa malamin jami'ar MAUN dake Kano da aka lakadawa na jaki saboda zargin neman matar aure suna ya nemesu. Matan sun bayyana hakane ga shahararren mawallafin labarai na kafafen sada zumunta, watau, Abis Fulani. Saidai Abis Fulani yace ba zai wallafa zargin da wadannan matan suka kai masa ba inda yace baya son shafinsa ya zama wajan tone-tonen Asirin mutane. Yace matan su kaiwa hukumar makarantarsu korafi. Sannan ya bayyana cewa jami'ar MAUN dake Kano ta fitar da bayanai cewa malamin da aka lakadawa dukan ya daina mata aiki dama aikin wucin gadi ne ya mata. https://www.tiktok.com/@abis_fulani/video/7660643441885416736?_r=1&_t=ZS-97uiA4u0IHl
Kalli Bidiyon: Sumbatar juna da Gfresh Al-amin da matarsa Sadiya Haruna suka yi a bainar jama’a ya jawo cece-kuce

Kalli Bidiyon: Sumbatar juna da Gfresh Al-amin da matarsa Sadiya Haruna suka yi a bainar jama’a ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
An ga Taurarun Tiktok, Sadiya Haruna da Gfresh Al-amin suna Bidiyo a tsakaninsu bayan da yace ya mayar da ita. A baya dai an ga yanda Gresh ya taro matar tasa a Filin jirgi bayan ta dawo daga Umara. A wannan sabon Bidiyon an gansu ne suna cin abinci a wani gidan sayar da abinci wanda Gfresh yace kyauta aka basu. Sannan kuma an ga suna sumbatar juna a bainar jama'a wanda hakan ya jawo cece-kuce https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7660647942029757703?_r=1&_t=ZS-97ugOjQDavV
Kalli Bidiyon: Ina neman mijin aure, kuma zan bashi jari da Sadaki, idan ka matsa sai ka biya sadaki, Salati kawai nake son kawa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) inji Wanan matar

Kalli Bidiyon: Ina neman mijin aure, kuma zan bashi jari da Sadaki, idan ka matsa sai ka biya sadaki, Salati kawai nake son kawa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) inji Wanan matar

Duk Labarai
Wannan wata matace data dauki hankula bayan data fito ta bayyana cewa, tana neman mijin aure. Matar tace duk me sonta idan bashi da sana'a zata bashi jari. Sannan zata bashi sadaki inda tace amma idan ya dage sai ya biya sadaki, abinda kawai take son ya biya shine ya wa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Salati. Ta bayyana hakane a shafinta na Tiktok inda tace duk wanda ke sonta ya ajiye mata lambar wayarsa a comment. https://www.tiktok.com/@mominjss/video/7660525260772691207?_r=1&_t=ZS-97ueHJXhJ4v
Ta kusa da Atiku, Dr. Aslam Aliyu data ce ta koma APC tace a daina damunta idan ba haka ba zatawa Atiku tonon silili

Ta kusa da Atiku, Dr. Aslam Aliyu data ce ta koma APC tace a daina damunta idan ba haka ba zatawa Atiku tonon silili

Duk Labarai
Dr. Aslam Aliyu wadda ta kusa da Atiku Abubakar amma yanzu ta fice daga jam'iyyar ADC ta koma jam'iyyar APC tace yaransa su daina damunta. Tace Atiku Abubakar yaci amanarta ne shiyasa ta barshi. Tace kuma da ake zaginta dan ta bar jam'iyyar ADC, bata zagi Atiku ba, dan Atiku daya koma APC me yasa shi ba'a zaginsa? Tace kuma na kusa da Atiku basu kaunarsa. https://www.tiktok.com/@expressmediahausa/video/7660623483247856914?_r=1&_t=ZS-97uVdjS2MUf
Kalli Bidiyon: Malamai da yawa a Arewa addinin karya suke koyawa, ba haka ake Musulunci a sauran kasashen Duniya ba>>Inji Soja Boy

Kalli Bidiyon: Malamai da yawa a Arewa addinin karya suke koyawa, ba haka ake Musulunci a sauran kasashen Duniya ba>>Inji Soja Boy

Duk Labarai
Tauraron mawakin Hausa, Soja Boya ya caccaki malaman addinin Addinin Musulunci inda yace addinin Karya suke koyarwa mutanen Arewa. Yace irin yadda Malamai ke koyar da Musulunci a Najeriya babu inda ake koyar da Musulunci haka a kasashen Duniya hatta kasashen Larabawa. Yace to shin Shi bahaushe yana tunanin shi kadaine zai shiga Aljanna kenan. Soya boy yace duk malamin da ya kara ce masa ba'a zo zama Duniya ba to uwarsa suka zo yi Duniya? Sannan yace kwanannan zasu fara cin uwar malamai. https://www.tiktok.com/@officialsojaboyy/video/7660652503427501332?_r=1&_t=ZS-97uQR1RDrYS