Wannan matashiyar ta dauki hankula a kafafen sada zumunta saboda yanda aka ganta da wani Dattijo suna soyayya.
An yi ta bayyana mabanbanta ra'ayoyi akan Bidiyon nasu.
https://twitter.com/Abu_Jawaadd/status/2099019552906526835
Ambaliyar ruwa ta yi barna a jihar Anambra inda ta lalata motoci da dukiyoyin Al'ummar jihar.
An ga mutanen da suka yi asara suna fitowa suna bayyanawa Duniya irin asarar da suka tafka.
https://twitter.com/yabaleftonline/status/2098674078911438998
https://twitter.com/instablog9ja/status/2098672603569242382
Wani magidanci ya dauki hankula a Abuja bayan kama Kwarto da matarsa Banex Plaza.
An ga magidancin suna fada shi da Kwarton inda jama'a suka shiga tsakani.
Lamarin ya dauki hankula inda ake ta Mihawa akai.
https://twitter.com/instablog9ja/status/2098850974802530767
Wannan wani matashine yake tsotsar kafar masoyiyarsa.
An gansu tare a cikin mota yana tuki inda take tura masa kafarta shi kuma yana kama kafar yana tsotsa.
Da yawa sun ce ba zasu iya aikata hakan ba.
Wasu kuma sun bayyana hadarin take tattare da hakan musamman idan kafarta bata da tsafta hakanan gangancine tunda yana tukine.
https://twitter.com/Legend6p/status/2098799776586191119
Tinubu saboda bakin hali irin naka, ka kashe Biliyan 37 wajan tafiye-tafiye amma kana ce mana mu kara hakuri.
Insha Allah ba zaka ghamaa da Duniya lafiya ba.
Ku kuma 'yan Najeriya in kun ga dama ku ci gaba da zaben barayi ku kuka sani.
Tinubu na da tarihin laifi.
Shugaban ma'aikatansa na da tarihin laifi.
Shugaban kula da tattalin arzikinsa nada Tarihin Laifi ba dole su yi ta wadaka da dukiyar kasa ba.
Inji Wannan matar bayerabiya daka dauki hankula a kafafen sada zumunta.
https://twitter.com/originalproflle/status/2098898477623255414
Wannan wani matashine da aka kama a Kano da shigar mata inda yaje zai shiga dakin kwanan mata na makarantar FCE Kano.
Bayan kamashi aka mikashi wajan hukuma, yace sunansa Umar Aliyu kuma daga Goron Dutse yake a Kano.
Yace kayan kakarsa ne yayi amfani dasu.
https://twitter.com/Annour_gaya/status/2098871079385088494
Wannan wani dan Najeriya ne da yaje filin Stanford Bridge na Chelsea dan kallon wasansu sanye da malinmalun.
Saidai chelsea din basu yi nasara ba.
An ganshi cikin damuwa.
https://twitter.com/dammiedammie35/status/2098812209061064749
Nan Mutanen Unguwar Rigasa dake jihar Kadunane suka fito zàngà-zàngà suna bayyana rashin jin dadinsu akan Ordinary President Ahmad Isa game da kalamansa akan Shugaban 'yan banga na unguwar Aminu Bolo.
Sun ce suna tare Aminu Bolo
https://twitter.com/KafinHausaa/status/2098736387503571446
'Yansandan Najeriya sun fara koyan yaren kasar China.
An gansu a wani Bidiyo wata 'yar kasar China na koya musu yaren har suna ta Dariya.
Rahoton yace ana koya musu ne kasancewar 'yan China sun yi yawa a Najeriya.
https://twitter.com/Uno_009/status/2098724360823406918