Saturday, February 14
Shadow
Kalli Bidiyon: Abinda Wannan mahaifin yawa ‘ya’yansa da ya dauki hankula sosai

Kalli Bidiyon: Abinda Wannan mahaifin yawa ‘ya’yansa da ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Wannan mahaifin ya sayawa 'ya'yansa Wardrobe ta saka kaya da suka dade suna tambayarsa ya siya musu. Ya nuna yanda kayan yaran nasa ke zube a kasa inda yace sun dade suna rokonsa ya sai musu inda zasu rika saka kayansu. Yace ya dade yana son ya sai musu sai aka yi sa'a wani abokinsa yana son sayarwa ya kirashi yace ya saya. An ga yaran nata murna bayan da suka dawo daga makaranta suka tarar da mahaifinsu ya saya musu Wardrobe din. https://twitter.com/i/status/2012415996615700912
Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Kebbi tare da soja me guntulen Hannu da ya jawo cece-kuce sosai

Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Kebbi tare da soja me guntulen Hannu da ya jawo cece-kuce sosai

Duk Labarai
A ranar Tunawa da 'yan mazan jiya, Gwamnan jihar Kebbi, Nasiru Idris ya hadu da wani soja da ya rasa hannunsa a wajan aiki. An gabatar da sojan a wajan gwamnan, inda gwamnan yace a yiwa sojan hannun Roba, inda yace a masa me kyau, har yana tambaya duka nawa yake? https://twitter.com/i/status/2012100209048977895 Saidai wannan lamari ya jawo cece-kuce inda masu sharhi suka zargi gwamnan da rashin nuna tausai ga sojan musamman ganin cewa ya rasa hannun nasa ne wajan yiwa kasa Hidima. Masu Sharhin na ganin cewa ba maganar kudi kawai bace, ya kamata gwamnan ya nuna alhini da halin da sojan ke ciki.
Kalli Hotuna:Dan gidan Ministan Ayyuka, Osborn Umahi ya fito takarar kujerar shugaban karamar hukuma

Kalli Hotuna:Dan gidan Ministan Ayyuka, Osborn Umahi ya fito takarar kujerar shugaban karamar hukuma

Duk Labarai
Dan gidan Ministan ayyuka, Osborn Umahi ya fito takarar neman kujerar shugaban karamar hukumar. Ya fito ne neman takarar kujerar Karamar hukumar Ohaozara ta jihar Ebonyi. Magoya bayansa ne suka rakashi Ofishin APC inda ya sayi fom din takarar akan Naira Miliyan 30. Dama dai a baya yawa mahaifinsa shugaban yakin neman zabe sannan kuma gwamnan jihar Ebonyi na yanzu, Francis Nwifuru ya bayyana shi a matsayin dan takararsa
Wanda suka tsayawa Malami aka bayar da belinsa na son su janye

Wanda suka tsayawa Malami aka bayar da belinsa na son su janye

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wadanda suka tsayawa Tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami aka bayar da belinsa na son janyewa. Hakan yasa lauyoyin Malamin suka je a yau, Juma'a sika samu babban Alkalin kotun tarayya suka nemi ya taimaka a saki Malami daga gidan yarin Kuje. Saidai Sahara Reporters data ruwaito lamarin tace, An yi bayanin ne a sirri ba'a san ba'a bari kowa yasan abinda aka tattauna ba.