Tuesday, December 23
Shadow
Zan tsaya takarar shugaban kasa a 2027 – Peter Obi

Zan tsaya takarar shugaban kasa a 2027 – Peter Obi

Duk Labarai
Zan tsaya takarar shugaban kasa a 2027 – Peter Obi. Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, ya tabbatar wa magoya bayansa cewa zai tsaya takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2027, kuma ba zai yi fiye da wa’adi guda ba idan ya ci zabe. Mista Obi ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Peter Obi Media Reports, Ibrahim Umar, ya fitar a ranar Litinin a Abuja. Tsohon dan takarar shugaban kasar ya tabbatar da cewa yana cikin tattaunawar kafa kawancen jam’iyyu, yana mai cewa burinsa shi ne ceton Najeriya daga halin da ta tsinci kanta. “Ban taba shiga wata tattaunawa kan hadin gwiwar tikitin takara da kowa ba, har da Atiku,” inji shi. “Idan za a samu wata yarjejeniya da za ta takaita wa’adin mulkina zuwa shekaru hudu...
Kakanninmu asali ƴan Najeriya ne – Shugabar Majalisar Dattawan Saint Lucia ta shaida wa Tinubu

Kakanninmu asali ƴan Najeriya ne – Shugabar Majalisar Dattawan Saint Lucia ta shaida wa Tinubu

Duk Labarai
Kakanninmu asali ƴan Najeriya ne – Shugabar Majalisar Dattawan Saint Lucia ta shaida wa Tinubu. Shugabar Majalisar Dattawan kasar Saint Lucia, Alvina Reynolds, ta bayyana karfin alaƙa ta asali tun kakanni tsakanin ƙasar da Najeriya. Reynolds ta buga misali da bayanan ƙidayar al'umma na Biritaniya da aka gudanar a tsibirin a 1815, inda aka gano cewa yawancin mutanen Saint Lucia na da asali daga Najeriya. Ta bayyana hakan ne yayin tarbar Shugaba Bola Tinubu a zama na hadin gwiwa na majalisun dokoki biyu na kasar Saint Lucia a jiya Litinin. Bayani game da wannan zaman hadin gwiwa, ta fito ne a wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya fitar ga manema labarai a jiya Litinin a birnin Abuja. “Daga cikin bayi 16,282 da aka kawo Saint Lucia a waccan shek...
An gurfanar da matashin da ya hau kan allon talla saboda dan Tiktok a kotu

An gurfanar da matashin da ya hau kan allon talla saboda dan Tiktok a kotu

Duk Labarai
An gurfanar da matashin da ya hau kan allon talla saboda dan Tiktok a kotu. Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta gurfanar da wani matashi mai shekaru 19 mai suna Ibrahim Abubakar, bisa laifin yunkurin kashe kansa, bayan da ya hau wata babban karfen talla a Kano ya kuma yi barazanar yin tsalle daga sama, yana danganta hakan da rashin ganin fitattun taurarin TikTok da yake kauna. Abubakar, dan asalin jihar Adamawa, ya tayar da hankula a ranar Litinin a Gadar Lado da ke kan titin Zariya, lokacin da ya hau saman wani Babban allon talla ya kuma yi ikirarin zai kashe kansa idan har fitattun masu TikTok da yake bibiyarsu ba su bayyana a wurin ba. A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma’a, Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yansanda a jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar d...
Kalli yanda Dangote ya raka gawar Kawunsa Aminu Dantata zuwa Madina

Kalli yanda Dangote ya raka gawar Kawunsa Aminu Dantata zuwa Madina

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya raka gawar kawunsa, Aminu Dantata daga Abu Dhabi kasar UAE zuwa Birnin Madina na kasar Saudiyya. Aminu Dantata ne daya daga cikin kawun Dangote Dangote na karshe da suka rage masa. https://twitter.com/SasDantata/status/1939963458931376381?t=OVEul28Z6bHYsZCZFuO5rw&s=19 Bayan sallar la'asar a kasar Saudiyya da misalin karfe 1:30 a Najeriya ne za'a yi jana'izar Marigayin.
Da Duminsa: An bayyana lokacin da za’awa gawar Marigayi Aminu Dantata sallah a Madina

Da Duminsa: An bayyana lokacin da za’awa gawar Marigayi Aminu Dantata sallah a Madina

Duk Labarai
Bayan sallar La'asar a ranar Talata ne ake sa ran za a gudanar da jana'izar fitaccen attajirin nan Alhaji Aminu Ɗantata a masallacin Madina. Mustapha Junaid, mataimaki na musamman ga marigayin ya shaida wa BBC cewa shirye-shirye sun kammala domin gudanar da jana'izar. "Alhamdu lillah an ɗauki marigayi Alhaji Aminu Ɗantata daga filin jirgi na Madina kuma yanzu haka za a je Shakzura inda a nan ne za a ƙarasa shirya shi kafin daga bisani a kai shi haramin Madina domin gudanar da sallah kamar yadda hukumomin Saudiyya suka amince." In ji Mustapha Junaid. A ranar Asabar ne shahararren ɗankasuwa Aminu Ɗantata ya rasu yana da shekara 94 da haihuwa a shekarar miladiyya. A shekarar Hijira (ta Musulunci) kuma, ya rasu yana da shekara 97, kamar yadda sakatarensa Mustapha Abdullahi ya shaid...
Da gaske Sarki Sanusi II ne zai yiwa Mariya Aminu Dantata sallar Gawa? Ji bayani dalla-dalla

Da gaske Sarki Sanusi II ne zai yiwa Mariya Aminu Dantata sallar Gawa? Ji bayani dalla-dalla

Duk Labarai
Rahotanni nata yawo a kafafen sada zumunta inda ake yada cewa, sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ne zai yiwa gawar Marigayi Aminu Dantata Sallah a birnin Madina. Hakan na zuwane yayin da rahotanni ke cewa, Sarki Aminu Ado Bayero ma yace Santata ya bar masa wasiyyar cewa shine zai masa sallah. A yanzu dai gawar marigayi Aminu Dantata ta isa Birnin Madina kuma ana jiran mahukunta birnin ne su bayyana lokacin da za'a masa sallah. A hukumance, ba'a sanar da wanene zaiwa gawar Marigayi Aminu Dantata Sallah ba.
Kalli Bidiyo Da Duminsa: Gawar Marigayi Dantata ta Isa Madina da safiyar yau

Kalli Bidiyo Da Duminsa: Gawar Marigayi Dantata ta Isa Madina da safiyar yau

Duk Labarai
Rahotanni daga Madina birnin Ma'aiki na cewa, gawar marigayi Aminu Dantata ta isa birnin. Bayan Saukar Gawar Marigayi Alh Aminu Dantata Tareda da Iyalensa; Alh Tajudeen Dantata da Hassan Dantata da Yaya, Jikoki da Yan Uwa Da Abokan Arziki duk Suna Wannan Guri Domin Mika Marigayi zuwa ga Ma'aikatan Kula Da Makabartar Baki'ah Inda akesa Rai Zasuyi masa Suttura. Allah yajikan sa Da Rahma. https://twitter.com/GASHASHCOLLECT2/status/1939964376754057576?t=i0_KkOxpnECK4Dy5VN-ZiQ&s=19 Me magana da yawunsa yace zasu jira hukumomin Madina au basu lokacin da za'a masa sallah.
Kalli Bidiyo Da Duminsa: An Sàcè kanin Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare>>Inji Mahdi Shehu

Kalli Bidiyo Da Duminsa: An Sàcè kanin Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare>>Inji Mahdi Shehu

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Dan siyasa, Mahdi Shehu yace an sace kanin Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare. Ya bayyana hakane a shafinsa na X inda ya wallafa Bidiyon wani mutum da aka gani zagaye da 'yan Bindiga rike da muggan makamai yana fadar cewa uwarsu daya ubansu daya da Gwamnan jihar Zamfara. Mahdi dai yayi tambayar cewa shin ko Gwamnan zai biya kudin fansa. Ko kuwa zai yi sulhu da 'yan Bindigar? Kalli Bidiyon anan Babu dai wata sanarwa data tabbatar da cewa wannan mutumin dan uwa...
Matatar man Dangote ta kara rage farashin man fetur dinta

Matatar man Dangote ta kara rage farashin man fetur dinta

Duk Labarai
Matatar man fetur din Dangote ta rage farashin man fetur dnta inda a yanzu take sayar dashi akan Naira 840 maimakon 880 da yake a baya. Hakan na wakiltar ragin kaso 4.5. Bincike ya bayyana cewa Dangote ya rage farashin nasa ne bayan da farashin danyen man fetur ya fadi a kasuwar Duniya zuwa dala $67.50 daga Dala sama da $70 da yake a baya. Wasu sauran kamfanonin ma sun rage farashin man fetur din nasu kamar yanda Dangote yayi.
Shin wai ina Kwankwaso? Ana ta cece-kuce bayan da manyan mutanen Kano suka je jana’izar Aminu Dantata Madina amma ba’a ga Kwankwaso ba

Shin wai ina Kwankwaso? Ana ta cece-kuce bayan da manyan mutanen Kano suka je jana’izar Aminu Dantata Madina amma ba’a ga Kwankwaso ba

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Yayin da manyan mutanen jihar Kano suka hallara a Madina wajan jana'izar Marigayi Aminu Dantata, ana ta daga wuya dan ko za'a hango Kwankwaso amma ba'a ganshi ba. Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya jagoranci tawagar Gwamnan Jigawa da Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero zuwa jana'izar. Da yawa sun yi tsammanin za'a ga Kwankwaso a cikin tawagar amma ba'a ganshi ba. Hakan yasa ake ta cece-kuce akai. Wasu dai na ganin zuwan Abba Gida-Gida ya isa ya wakilci Kwankwa...