Thursday, December 18
Shadow
ABIN MAMAKI: Ji yanda ake zargin ‘Yan Ķasar Indiýa Sùn Ķori ‘Ýan Nijeriya Daga Nìjeriya

ABIN MAMAKI: Ji yanda ake zargin ‘Yan Ķasar Indiýa Sùn Ķori ‘Ýan Nijeriya Daga Nìjeriya

Duk Labarai
ABIN MAMAKI: 'Yan Ķasar Indiýa Sùn Ķori 'Ýan Nijeriya Daga Nìjeriya. Ɗan jarida Nasiru Zango ya rubuta yana mai cewa wannan hoto da kuke gani dake nuna wasu matasa biyu da 'yan sandan Nijeriya ke neman su ruwa a jallo ba kayan kowa suka sata ba kuma ba su yiwa kowa komai ba, babban laifin su bai wuce kasancewar su jajirtattun matasa masu neman abin kan su ba ta hanyar da dokar Nijeriya ta tanada, sai kuma watakila dan sun kasance masu karamin karfi da suka ki yadda wani babban kamfani ya zo har kasar su yana kokarin murkushe su ba. Fiye da shekara kenan wani babban kamfani na 'yan asalin Indiya ya yi karar wadannan matasa wadanda sune suke da mallakin kamfanin ganyen shayin Y and Z kan cewar sun satar musu samfurin ganyen shayin su (kamar yadda Coca Cola suka taba yin karar Pop C...
Ku Godewa Allah: Rababa muke sayar muku da man fetur idan aka kwatanta da farashin man fetur din a sauran kasashen Africa>>Dangote ya gayawa ‘yan Najeriya

Ku Godewa Allah: Rababa muke sayar muku da man fetur idan aka kwatanta da farashin man fetur din a sauran kasashen Africa>>Dangote ya gayawa ‘yan Najeriya

Duk Labarai
Babban Attajirin Najeriya wanda ya mallaki matatar man fetur mafi girma a Nahiyar Africa, Aliko Dangote yacewa 'yan Najeriya suna cikin Alheri da sa'a dan kuwa suna sayen man fetur a farashi kasa da wanda sauran kasashen Africa ke saye. Dangote yace farashin man fetur a Najeriya yana ana sayar dashi ne kaso 55 cikin 100 kasa da farashin da ake sayarwa a sauran kasashe. Watau 'yan Najeriya na siyan man fetur din a farashib kaso 45 cikin 100 idan aka kwatanta da sauran kasashen Africa. Dangote yace kuma matatar mansa ta taimaka wajan rage farashin man fetur din a Najeriya daya tsaya a farashin tsakanin Naira 815 zuwa Naira 820 akan kowace lita. Dangote ya bayyana hakanne a yayin da shugaban Kungiyar ECOWAS, Dr Omar Touray da tawagarsa suka kai mai ziyara matatar tasa. Yace za...
Matar Wannan mutumin ta ràsù a ambaliyar ruwan data faru a Mokwa jihar Naija, hakanan jaririnsa da ‘yan uwansa 7 duk sun ràsù da kayan jikinsa kawai ya tsira

Matar Wannan mutumin ta ràsù a ambaliyar ruwan data faru a Mokwa jihar Naija, hakanan jaririnsa da ‘yan uwansa 7 duk sun ràsù da kayan jikinsa kawai ya tsira

Duk Labarai
Wannan mutumin me suna Adamu Yusuf ya rasa iyalansa guda 9, matarsa daya da jaririn dansa da 'yan uwansa 6 a ambaliyar ruwan da ta faru a Mokwa dake jihar Naija. Shi ya fitone daga Tiffin Maza daya daga cikin kauyukan da lamarin ya fi shafa. Yace da suka ji ruwan, sun fito waje inda yake kowa ya rike hannun kowa yace amma da ruwan yayi karfi sai ya tarwatsasu, yace yana ji yana gani haka ruwan ya tafi da iyalinsa. Yace shima Allah ne ya tseratar dashi saboda ya iya ruwa. Yace kayan dake jikinsa ma taimako aka bashi.
Tsohon Ministan Muhalli lokacin Buhari ya bar jam’iyyar APC

Tsohon Ministan Muhalli lokacin Buhari ya bar jam’iyyar APC

Duk Labarai
Tsohon Ministan Muhalli a zamanin Mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, watau Mohammed Abdullahi ya bar jam'iyyar APC. A karkashin Mulkin Buhari an nada Muhammad Abdullahi a matsayin karamin Ministan Kimiyya da Fasaha kamin daga baya aka mayar dashi ministan Muhalli. Ya bayyana barin jam'iyyar APC ne a wasikar da ya aikewa jam'iyyar reshen mazabar sa dake Uke ward karamar hukumar Karu, Jihar Nasarawa. Ya bayyana dalilai na kashin kansa ne suka sa ya bar jam'iyyar inda yace ya gode da damar da aka bashi ta gina jam'iyyar tare dashi. A baya kamin ya zama Ministan, ya rike mukamai da yawa a jihar Nasarawa ciki hadda babban sakataren gwamnati da Kwamishina.
Kasashen Larabawa sun yi Allah wadai da kasar Israyla saboda hanasu kaiwa Falasdiynawa ziyara da ta yi

Kasashen Larabawa sun yi Allah wadai da kasar Israyla saboda hanasu kaiwa Falasdiynawa ziyara da ta yi

Duk Labarai
Ministocin harkokin wajen ƙasashen Larabawa sun bayyana rashin jin daɗinsu ga gwamnatin Isra'ila, game da rashin amincewa da tawagar ƙungiyar ƙasashen ta ziyarci yankin da aka mamaye a Gaɓar Yamma da kogin Jordan don tattaunawa da shugaban Falasɗinawa. A wani taron manema labarai, ministan harkokin wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan Al Sa'ud, ya ce matakin da Isra'ila ta ɗauka kamar watsi ne da tayin zaman lafiya. A ranar Asabar wani jami'in Isra'ila ya ce batun samar da ƙasar Falasɗinu ne manufar ziyarar. Cikin wata sanarwar haɗin-gwiwa, ƙasashen Masar da Qatar sun ce za su ruɓanya ƙoƙarinsu don a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza. Shugaban ƙungiyar ƙasashen Larabawa da ministoci huɗu sun gana da shugaban Falasɗinawa Mahmoud Abbas ta kafar Intanet....
Mutanen da ambaliyar ruwa ta kàshè a Neja sun kai 200, in ji jami’ai

Mutanen da ambaliyar ruwa ta kàshè a Neja sun kai 200, in ji jami’ai

Duk Labarai
Mutanen da ambaliyar ruwa ta kashe a garin Mokwa na jihar Neja sun kai sama da 200, in ji jami'ai. Akwai wasu kusan 500 da ba a gani ba har yanzu, yayin da ake ci gaba da aikin ceto. Mataimakin shugaban karamar hukumar Mokwa, Musa Kimboku ya shaida wa BBC cewa an dakatar da aikin ceto saboda hukumomi sun yi imanin cewa watakila babu wanda ya rage da rai. Ambaliyar wadda aka bayyana cewa ba a ga irinta ba tsawon shekara 60, ta lalata gidaje a anguwannin Tiffin Maza da Hausawa, bayan tafka mamakon ruwan sama ranar Laraba da daddare. Hukumomi za su fara tono gawawwaki da aka binne don bincike, a wani yunkuri na kauce wa yaɗuwar cutuka, kamar yadda Maigarin Mokwa Muhammad Aliyu ya bayyana. Mazauna yankin sun bayyana cikin kaɗuwa yadda suna kallo suka rasa ƴan uwansu da gidajensu...
Kalli Bidiyo yanda sojojin Israyla suka budewa Falasdiynawa wuta suka kàshè 22 yayin da suka taru suna karbar Tallafin Abinci

Kalli Bidiyo yanda sojojin Israyla suka budewa Falasdiynawa wuta suka kàshè 22 yayin da suka taru suna karbar Tallafin Abinci

Duk Labarai
Rahotanni daga Falasdinu na cewa, Sojojin kasar Israela, IDF sun budewa taron Falasdiynawa wuta a yayin da suka taru suke karbar tallafin abinci. Lamarin yayi sanadiyyar mutuwar mutane akalla mutane 22. Wakilin majalisar Dinkin Duniya ya bayyanawa Kamfanin dillancin labaran AFP cewa raba kayan tallafi a gaza ya zama tarkon Mutuwa. Kungiyar bayar da agaji ta Red Cross ta tabbatar da faruwar lamarin. Saidai wata gidauniyar agaji a Gaza tace rahoton bashi da inganci. Kalli Bidiyon anan
Ma’aikatan Shari’a zasu tsunduma yajin aikin sai mama ta gani gobe, Litinin

Ma’aikatan Shari’a zasu tsunduma yajin aikin sai mama ta gani gobe, Litinin

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Ma'aikatan shari'a na Najeriya karkashin Kungiyarsu ta (JUSUN) sun nace akan tafiya yajin aiki gobe, Litinin, 2 ga watan Mayu. Ma'aikatan bangaren babbar kotun tarayya ne zasu tafi yajin aikin inda bangaren kotun Koli suka fasa shiga yajinnaikin. Wata majiya tace shugaban hukumar DSS ya zauna da ma'aikatan tsawon awanni 4 amma duk da haka sun ce ba zasu fasa tafiya wannan yajin aikin ba. Sakataren kungiyar, Comrade Mohammed Isah yace zasu fara yajin aikin gobe Litinin inda yace yana kiran duka ma'aikatansu da su zauna a gida kada su je wajan aiki. Saidai yace a goben ma akwai wani zama sa za'a sake yi.
Tsare-tsaren Gwamnatin Tinubu ya jefa Mutanen Najeriya cikin matsanancin Talauci>>Inji Janar Buratai

Tsare-tsaren Gwamnatin Tinubu ya jefa Mutanen Najeriya cikin matsanancin Talauci>>Inji Janar Buratai

Duk Labarai
Tsohon shugaban sojojin Najeriya, Janar Tukur Yusuf Buratai ya bayyana cewa, Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta jefa 'yan Najeriya cikin matsin talauci. Ya bayyana hakane a wajan taron zagayowar ranar haihuwar tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi. Yace gwamnatocin baya a hankali suka rika jefa 'yan Najeriya cikin talauci amma Gwamnatin Tinubu, Lokaci guda ta jefa mutane saboda tsare-tsaren ta data gudanar masu tsauri. Saidai yayi fatan nan da shekaru biyu masu zuwa a samu saukin rayuwa wanda yace idan ba haka ba, akwai matsala.