Wednesday, May 21
Shadow

Yadda ake fara soyayya

Duk Labarai
A addinance, idan ka ga yarinya, Budurwa kana so, zaka fara zuwa wajan mahaifinta ne ka nemi izini. Idan kuma ba zaka iya zuwa ba kai tsaye, zaka iya aika magabatanka a nemar maka izini idan ba'a bayar da ita ba. Idan ka samu aka maka iso to aiki ya ganka. Anan ne kai kuma aiki ya rage gareka ka samu hanyar da zaka yi nasara soyayyarka ta shiga zuciyarta. Abubuwan da zaka rika yi dan jan hankalinta: Ka rika yin kwalliya sosai idan zaka je wajenta. Ka rika saka turare. Ka wanke baki. Ka rika bata labarin abinda bata sani ba. Ka rika mata kyauta. Ka rika kokarin sata dariya. Ka mayar da ita abokiyarka, ka rika neman shawarar ta. Wannan zai sa ka shiga zuciyarta sosai kuma itama ta ji tana sonka.
MASANA’ANTAR KANNYWOOD WAJE NE NA GYARA TARBIYYA BA GURƁATA WA BA, CEWAR MARYAM SANI

MASANA’ANTAR KANNYWOOD WAJE NE NA GYARA TARBIYYA BA GURƁATA WA BA, CEWAR MARYAM SANI

MARYAM SANI
Wata sabuwar Jaruma a masana'antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, Maryam Muhammad Sani ta bayyana Kannywood ɗin a matsayin wata masana'anta wacce ake faɗakarwa da gyaran tarbiyyar al'umma ba wai ɓata tarbiyya ba. Maryam ta bayyana haka ne ta cikin wata tattaunawarta da Jaridar Dokin Ƙarfe TV inda ta ƙara da cewa "Na shigo masana'antar Kannywood ne domin ina da gudunmawar da zan bayar game da gyaran tarbiyyar al'ummar nan tamu". In jita. Maryam ta kuma ƙara da cewa "Bai kamata mutane suna ƙyamatar ƴan fim ba. Domin fim harka ce ta kawo cigaba da magance matsalar tsaro da raya al'adun Hausa Fulani". A cewar ta. Daga ƙarshe Malama Maryam ta kuma ƙara da cewa tarbiyya tana farawa ne tun daga gida, dan haka masana'antar Kannywood waje ne na koya tarbiyya ba ɓatawa ba". In ji ta....
Kalli Kuga: Kungiyar Hezbollah ta sanar da lalata babban makamin kasar Israela me suna Iron Dome da take amfani dashi wajan tare makaman da ake harba mata

Kalli Kuga: Kungiyar Hezbollah ta sanar da lalata babban makamin kasar Israela me suna Iron Dome da take amfani dashi wajan tare makaman da ake harba mata

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Yakin gaza da isra'ila
Kungiyar Hezbollah ta kasar Lebanon ta sanar da kaiwa babban makamin da kasar Israela take ji dashi wajan tare makaman da ake aika mata me suna Iron Dome. Hezbollah tace ta aikawa Iron Dome bamabamai ne wanda ya lalatashi da kuma kashe ko kuma raunata sojojin dake kula dashi.
Kalli Hoto: Tsohuwar ‘yar kwallon Najeriya da Tsohon Gwamnan Kaduna Malam Nasiru Ahmad ya dauki nauyinta zuwa kasar Amurka aka mata aiki ta koma Namiji na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan a mata karin aikin da zata rika haihuwa

Kalli Hoto: Tsohuwar ‘yar kwallon Najeriya da Tsohon Gwamnan Kaduna Malam Nasiru Ahmad ya dauki nauyinta zuwa kasar Amurka aka mata aiki ta koma Namiji na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan a mata karin aikin da zata rika haihuwa

Duk Labarai
Tsohuwar 'yar kwallon Najeriya, Iyabo Abade wadda yanzu Namiji ce da sunan James Johnson na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan ta samu ta rika haihuwa. Iyabo ta bugawa Najeriya was a tsakanin 1997 da 2000. Kuma a shekarar 2004 ne aka canja mata halitta a kasar Amurka ta koma Namiji. Tsohon ministan babban birnin tarayya a wancan lokacin, Malam Nasiru El-Rufai ne ya dauki nauyin aikin da aka mata. Saidai kamin kace wani abu, Ita dai Iyabo an haifeta ne a matsayin mata maza, watau tana da azzakari da farji irin na mata. Dan hakane ta zabi daya ko kuma aka duba wanda yafi karkata aka gano Namiji ne kuma aka mata aiki ta koma cikakken Namiji. Saidai tana bukatar a kara mata aiki dan ta samu ta rika haihuwa.
Akwai yiyuwar a yi fama da wahalar man fetur yayin da kungiyar NUPENG ke shirin bin kungiyar kwadago itama ta yi yajin aiki

Akwai yiyuwar a yi fama da wahalar man fetur yayin da kungiyar NUPENG ke shirin bin kungiyar kwadago itama ta yi yajin aiki

Siyasa
Kungiyar ma'aikatan man fetur ta NUPENG ta umarci membobinta da su shiga yajin aikin sai mama ta gani wanda za'a fara a gobe Litinin. Sakataren Kungiyar, Mr Afolabi Olawale ne ya bayyana haka inda yace kungiyar tasu zata bi umarnin yajin aikin. Kungiyoyin NLC da TUC dai sun bayyana aniyar shiga yajin aiki a gobe litinin wanda sai abinda hali yayi kan neman gwamnati ta kara mafi karancin Albashi. Wannan mataki na NUPENG dai zai iya jefa da yawa daga cikin 'yan Najeriya cikin matsalar wahalar man fetur.

Idan aka biya ma’aikata mafi karancin Albashin da suke nema na Naira N494,000 sauran mutanen Najeriya zasu shiga wahala>>Ministan Yada Labarai

Siyasa
Ministan yada labarai, Mohammed Idris ya bayyana damuwa kan bukatar kungiyar NLC ta a biyasu mafi karancin Albashi na Naira N494,000. Ministan yace idan aka biya wannan mafi karancin Albashin da kungiyar NLC take nema, za'a rika kashe Naira N9.5 trillion wajan biyan Albashi. Ya kara da cewa kuma hakan zai jefa rayuwar sauran 'yan Najeriya miliyan 200 cikin wahala. A zama na karshe dai da aka yi tsakanin kungiyar ta Kwadago da Gwamnati an tsaya ne akan gwamnati zata biya Naira Dubu 60 a matsayin mafi karancin Albashi wanda kungiyar Kwadagon tace bata yadda ba. Hakan yasa kungiyar tace tunda dai ba'a cimma matsaya tsakaninta da gwamnati ba, zata shiga yajin aikin sai mama ta gani daga ranar Litinin dinnan me zuwa.
Hukumar Wutar lantarki ta Abuja zata yankewa hedikwatar Sojoji dana ‘yansanda wuta saboda bashi

Hukumar Wutar lantarki ta Abuja zata yankewa hedikwatar Sojoji dana ‘yansanda wuta saboda bashi

Siyasa
Hukumar wutar lantarki ta Abuja ta bayyana cewa, zata yankewa manyan ma'aikatu da yawa wuta saboda bashin kudin wutar da ake binsu. Ta bayyana cewa, daga cikin hukumin da ake bin bashin akwai hukumar sojojin, dana 'yansanda da ma'aikatar mata ta tarayya, da jihar Kogi, da ma'aikatar Ilimi, da ma'aikatar masana'antu. Hukumar tace ba wata ma'aikata da zata dagawa kafa zata yanke mata wuta. Hakan na kunshene a cikin sanarwar da hukumar wutar ta fitar.

YANZU-YANZU: Real Madrid Ta Ci Kofin Zakarun Turai Karo Na 15 Bayan Ta Yi Nasara Kan Dortmoumd Da Ci 2-0

Kwallon Kafa
Kungiyar Real Madrid ta lashe kofi na 15 bayan da ta doke Borussia Dortmund da ci 2-0 a wasan karshe da suka buga a filin wasa na Wembley. Dani Carvajal da Vinicius Jr ne suka ci kwallayen 2. Tsohon dan wasan Real Madrid din kuma kocinta, Zinedine Zidane ne ya kai kofin filin: Kungiyar Borussia Dortmund ta gayyaci Jurgen Klupp ya kalli wasansu. Shine dai ya kaisu wasan karshe na gasar da suka buga a shekarar 2013. Mahaifi da mahaifiyar Jude Bellingham da dan uwansa sun je kallon wasan. https://twitter.com/footballontnt/status/1796957357852832007?t=AfUBdCBVKdBJiz6B_0kChQ&s=19 Hakana mawakin Amurka Jay Z ma ya je kallon wasan: https://twitter.com/ChampionsLeague/status/1796973390743351387?t=l4Xncg675YAq4gnq5hRRRg&s=19 An samu wani da yayi kutse a ...