Friday, December 5
Shadow
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ta tabbata Tshageran Daji Sunm aikha da Janar Muhammed Uba Lakhira

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ta tabbata Tshageran Daji Sunm aikha da Janar Muhammed Uba Lakhira

Duk Labarai
Rahotanni sun tabbatar da cewa, Mayakan Kungiyar ÌŚWÀP a jihar Borno sun kama tare da Hallaka Janar din sojan Najeriya me suna Brigadier General Muhammed Uba. Rahotanni a baya sun ce ya tsere daga hannunsu bayan sun yiwa tawagarsa harin kwantan Bauna suka kamashi. Hukumar soji ta bayar da tabbacin cewa, ya koma sansaninsa a baya. Saidai Kungiyar dake Ikirarin jìhàdì ta wallafa hotunansa sannan ta sanar da cewa ta halakashi.
Muna baiwa shugaba Tinubu da sauran ‘yan Najeriya hakuri saboda munsan mun baku kunya, sau biyu kenan Super Eagles na kasa zuwa gasar cin kofin Duniya>>Inji Hukumar kwallon Najeriya, NFF

Muna baiwa shugaba Tinubu da sauran ‘yan Najeriya hakuri saboda munsan mun baku kunya, sau biyu kenan Super Eagles na kasa zuwa gasar cin kofin Duniya>>Inji Hukumar kwallon Najeriya, NFF

Duk Labarai
Hukumar kwallon kafa ta Najeriya, NFF tace tana baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da sauran 'yan Najeriya hakuri saboda fitar da Super Eagles da kasar Dr. Congo ta yi a wasan neman cancantar zuwa buga gasar cin kofin Duniya na shekarar 2026. NFF tace lamarin abin takaicine matuka domin sau biyu kenan a jere tana kasa zuwa gasar. Tace abin kunya ne amma tana neman afuwa. Kasar Dr. Congo tawa Najeriya ci 4-3 bayan an tashi 1-1 a jiya Lahadi wanda hakan ya hana Najeriya damar kaiwa ga gasar cin kofin Duniya na shekarar 2026.
Kalli Bidiyo: Ana ta sukar Malam Aminu Ibrahim Daurawa ciki hadda ‘yan Izala saboda amsar da ya baiwa wata mata data tambayeshi halascin Shugabancin mata

Kalli Bidiyo: Ana ta sukar Malam Aminu Ibrahim Daurawa ciki hadda ‘yan Izala saboda amsar da ya baiwa wata mata data tambayeshi halascin Shugabancin mata

Duk Labarai
Malam Aminu Ibrahim Daurawa na shan suka kuma ciki hadda 'yan Izala bayan amsar da ya baiwa wata mata data masa tambaya kan halascin shugabancin mata. Malam ya bayyana mata cewa akwai inda Matan zasu iya shugabanci zata iya tsayawa anan. https://www.tiktok.com/@daudakahutarara/video/7573390074709134599?_t=ZS-91TkbEgaOB6&_r=1 Saidai da yawa sun zargi malam da kin fitowa kai tsaye ya baiwa matar amsa inda suka zargeshi da yin kwana. Cikin masu sukar malam akan hakan hadda 'yan Izala. https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7573389723125828875?_t=ZS-91Tl5gyXUor&_r=1
Wallahi mafi yawanci masoya Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ‘yan WiyWiy ne, saboda mune zaka gani gaba-gaba a wajan Maulidi, da Wazifa da salati>>Inji Wannan Dan Wiywiy din

Wallahi mafi yawanci masoya Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ‘yan WiyWiy ne, saboda mune zaka gani gaba-gaba a wajan Maulidi, da Wazifa da salati>>Inji Wannan Dan Wiywiy din

Duk Labarai
Wani matashi mashayin wiywiy ya bayyana cewa su 'yan Wiywoy masoya manzon Allah ne, yace sune zaka gani gaba-gaba wajan wazifa, Maulidi da Salati. Matashin yace Munafiki baya shan Wiywiy kuma daga Aljannah aka kawo musu ita. Kalli Bidiyon bayaninsa a kasa: https://www.tiktok.com/@halifa_isco/video/7573402710284832056?_t=ZS-91ThwUf1B4L&_r=1
Kalli Bidiyon: Adam A. Zango ya Karbi Nasiha sannan yace ya gode bayan da aka yi kira gareshi ya daina Film da waka da rawa ta canja Sana’a

Kalli Bidiyon: Adam A. Zango ya Karbi Nasiha sannan yace ya gode bayan da aka yi kira gareshi ya daina Film da waka da rawa ta canja Sana’a

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Adam a Zango yayi godiya bayan da aka masa nasihar ya daina rawa da waka da film ya canja sana'a. Daya daga cikin masu nasiha a Tiktok ne ya jawo hankalin Adam A. Zango da cewa, Allah yana sonsa musamman ma yanda yafi jarabarsa fiye da sauran taurarin masana'antar Kannywood. Ya baiwa Adam A. Zango shawarar ya bude shago ya fara kasuwanci wanda yace idan ya saka Allah a gaba, zai ga nasara. Adam A. Zango ya bayyanawa matashin cewa ya gode da Nasiha. https://www.tiktok.com/@umarpitykhalid0/video/7572948017192455435?_t=ZS-91TejJjCHAH&_r=1
Jimullar Naira Tiriliyan 2.23 ‘yan Najeriya suka biya tsageran daji a matsayin kudin fhansa>>Inji Gwamnati

Jimullar Naira Tiriliyan 2.23 ‘yan Najeriya suka biya tsageran daji a matsayin kudin fhansa>>Inji Gwamnati

Duk Labarai
Hukumar kididdiga ta kasa, NBS ta bayyana cewa, Jimullar Naira Tiriliyan 2.23 'yan Najeriya suka biya a matsayin kudin fansa ga 'yan Bindigar daji. Hukumar tace an biya wadannan kudadene a tsakanin shekarun 2023 zuwa 2024. Hakanan bayanan sun ce an yi garkuwa da mutane sau Miliyan 2.2 a tsakanin wannan lokaci. Sannan a kalla kowane mutum an biya mai Naira Miliyan 2.7 a matsayin kudin fansarsa.
Daga yanzu karku kara yadda, Duk wanda aka yi Gharkiwa dashi ya biya kudin Fhansa ya kai Gwamnati kara ta biyashi kudinsa>>Inji Lauya Femi Falana

Daga yanzu karku kara yadda, Duk wanda aka yi Gharkiwa dashi ya biya kudin Fhansa ya kai Gwamnati kara ta biyashi kudinsa>>Inji Lauya Femi Falana

Duk Labarai
Babban lauya, Femi Falana(SAN) ya baiwa 'yan Najeriya shawarar cewa, kar su sake yadda daga yanzu duk wanda aka sake yin Garkuwa dashi ya biya kudin fansa, ya kai Gwamnati kara ta mayar masa da kudinsa. Yace dalili kuwa shine, Gwamnatin ta kasa bisa hakkin dake kanta na samar da tsaro ga 'yan kasa dan haka ya kamata a kalubalanceta. Ya bayyana hakane a wajan wani taro da ya gudana a jami'ar Yakubu Gowon University dake Abuja.
Fulani sun kora shanunsu cikin gonar shinkafata suka cinye rabin gonar, daga baya kuma suka je suka girbe sauran rabin>>inji Mal. Abdulhamid Abubakar

Fulani sun kora shanunsu cikin gonar shinkafata suka cinye rabin gonar, daga baya kuma suka je suka girbe sauran rabin>>inji Mal. Abdulhamid Abubakar

Duk Labarai
Malam Abdulhamid Abubakar ya bayyana cewa, Fulani makiyaya sun kora shanunsu cikin gonarsa ta shinkafa suka cinye rabin gonar. Yace daga baya kuma sun sake komawa suka girbe sauran gonar. https://twitter.com/_bahaushee/status/1990076142364012593?t=aNGcecigrV9-Eizb9PI8jw&s=19 Ya bayyana hakane a shafinsa na X inda jama'a ke ta masa Jaje.