Tuesday, January 13
Shadow
Tun tuni ya kamata in kawo Khàrì Najeriya amma na bari sai ranar Kirsimeti ne dan ya zama kyautar Kirsimeti>>Inji Trump

Tun tuni ya kamata in kawo Khàrì Najeriya amma na bari sai ranar Kirsimeti ne dan ya zama kyautar Kirsimeti>>Inji Trump

Duk Labarai
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, tun tuni ya kamata ya kai Najeriya hari, watau Rana Laraba. Amma yace ya jinkirta sai ranar Kirsimeti ne dan harin ya zama waa kyauta ta musamman. Ya bayyana hakane ranar Laraba, Kwana daya bayan kai harin Sokoto da Kwara wanda rahotanni suka ce ba kan 'yan Tà'àddà ya fada ba.
Khàrìn Da Amirka ta kawo Najeriya ba wani abu ne na musamman ba, Sojojin Najeriya ma zasu iya kai irinsa>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Khàrìn Da Amirka ta kawo Najeriya ba wani abu ne na musamman ba, Sojojin Najeriya ma zasu iya kai irinsa>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya bayyana cewa, harin da kasar Amurka ta kawo Najeriya bata yi kokari ba. Yace Sojojin Najeriya na da kwarewa da makaman da zasu iya kai irin wannan hari. Yace Yana kiran Gwamnati ta yanke hulda da Amurka sannan kuma idan taimakon yaki da ta'addanci take nema ta nema wajan kasashen Pakistan, Turkiyya ko China. Yace dalili kuwa shine shugaban kasar Amirka, Donald Trump a wulakance yake kallon Najeriya
Khàrìn da Amurka ta kawo Najeriya a yau zai ci gaba da wakana>>Inji Gwamnati  Tarayya

Khàrìn da Amurka ta kawo Najeriya a yau zai ci gaba da wakana>>Inji Gwamnati Tarayya

Duk Labarai
Ministan harkokin kasashen waje, Yusuf Tuggar ya bayyana cewa harin da Amurka ta kawo Najeriya ba shine na karshe ba. Yace akwai yiyuwar irin wadannan hare-haren anan gaba. Yace Najeriya suna hada kai da duk wata kasa da zata taimaka mata wajan yakar ta'addanci https://twitter.com/trigottista/status/2004483596648956302?t=E56lwh6m-vI2uA9DI4z0lg&s=19
Da Duminsa: Cikin Guraren da kasar Amurka ta kaiwa Khàrì a Najeriya a daren jiya hadda Masallaci

Da Duminsa: Cikin Guraren da kasar Amurka ta kaiwa Khàrì a Najeriya a daren jiya hadda Masallaci

Duk Labarai
Majiyoyi da suka haɗa da na gwamnatin jihar Kwara sun tabbatar da cewa an kai harin a wani ƙauye da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar Offa, inda a ƴan kwanaki wasu ƴan bindiga suka kai hari a coci wanda ya yi sanadiyya rasa ran mutum biyu sannan suka yi awon gaba da dama. Hotuna da BBC ta samu daga mazauna garin sun nuna yadda makamin ya faɗa kan gidajen al'umma a garin Offa inda ya rugurguza katangun wasu tsirarun gine-gine. Wani jami'in gwamnati ya ce al'amarin ya faru a wurare da dama a cikin garin na Offa da suka hada da filin Idi da wasu otal guda biyu da suka hada da Offa Central hotel da Solid Worth Hotel
Da Duminsa: Hukumomi a jihar Sokoto sun ce akan farar Hula Khàrìn Amurka ya fada

Da Duminsa: Hukumomi a jihar Sokoto sun ce akan farar Hula Khàrìn Amurka ya fada

Duk Labarai
HARE-HAREN AMURKA A SOKOTO: Ba mafakar ’yan ta’adda aka kai wa hari ba kusa da Asibiti harin ya fada –inji Dan Majalisar yankin Hon. Bashar Isah Daga Ayau News Dan Majalisar Dokokin Jihar Sokoto mai wakiltar Tambuwal ta Gabas yankin da abun ya faru, Hon. Bashar Isa Sarkin Yakin Jabo, ya musanta ikirarin cewa akwai mafakar ’yan ta’adda a yankin Jabo, inda aka ce sojojin Amurka sun kai hari a daren Alhamis. Ayau News ta ruwaito a hirarsa da DCL, Hon. Bashar ya ce wurin da abin ya faru kusa da Asibitin Jabo PHC ne, yankin da al’umma ke zaune lafiya, ba cikin daji ba, kuma babu wani bayani da ke nuna ayyukan ’yan ta’adda a yankin. Ya kara da cewa bayan harin, jama’ar yankin na cikin fargaba da tsoro, ganin cewa ba su san inda abin makamancin haka zai sake faruwa ba. Ya jaddada ...
Me ya kai Amurka Sokoto? Musulunci ne kawai suke son durkusarwa>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Me ya kai Amurka Sokoto? Musulunci ne kawai suke son durkusarwa>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya yi Allah wadai da harin da kasar Amurka tace ta kai jihar Sokoto. Malamin yace wannan harin A Borno 'yan tà'àddà suke me ya kai Amurka Sokoto? Yace wannan suna son su yaki musulunci ne kawai. Ya ce idan taimakoj tsaro Najeriya take nema kamata yayi ta nema a wajan kasashen Tirkiyya, Pakistan ko China. Yayi kiran Gwamnatin Najeriya ta yanke huldar tsaro da kasar Amurka.
Ka Mana Shiru, A gurin mu kuka koyi adinin Musulunci>>Wannan Balaraben ya gayawa dan Najeriya da yace bai kamata kasar UAE a taya Kiristoci murnar Kirsimeti ba

Ka Mana Shiru, A gurin mu kuka koyi adinin Musulunci>>Wannan Balaraben ya gayawa dan Najeriya da yace bai kamata kasar UAE a taya Kiristoci murnar Kirsimeti ba

Duk Labarai
Wani dan Najeriya ya ce bai kamata kasar UAE ta taya Kiristoci murnar Kirsimeti ba. Saidai wani Balarabe daga kasar ya mayar masa da martanin cewa, Ya rufe baki dan a wurinsu aka koyi addinin. https://twitter.com/Imamofpeace/status/2004439901572682218?t=3wFfsQ9Acyr1Uk3qsWVOkg&s=19