Sunday, April 5
Shadow
Ji yanda ‘yan Lùwàdì kewa kananan yara maza wayau suna aika musu hotunan Tsìràicìnsu, ana kasuwanci da hotunan ana sayarwa Turawa a Najeriya

Ji yanda ‘yan Lùwàdì kewa kananan yara maza wayau suna aika musu hotunan Tsìràicìnsu, ana kasuwanci da hotunan ana sayarwa Turawa a Najeriya

Duk Labarai
Wani abin ban mamaki da ya faru shine yanda aka gano wasu bata gari dakewa kananan yara maza wayau suna aika musu hotunansu tsirara. Yaran dai nantsakanin shekaru 14 zuwa 21 ne. Wasu daga cikinsu da saninsu ake aikata hakan saboda ana basu kudi, wasu kuma ba da saninsu ba saboda an musu wayau ne. Jaridar Punchng ta yi bincike akan lamarin kuma ta gano cewa ana amfani da kafafen sada zumunta ne irin su X ne wajan aikata wannan masha'a. Saidai ana ta kulle irin wadannan shafuka amma masu aikata wannan masha'a sai su kara bude wasu. Wasu yaran da a yanzu sun girma amma ana da Bidiyonsu suna cikin fargaba saboda a yanzu ana ta yada Bidiyon a kakafen sada zumunta wanda hakan yana zamar musu Abin Kunya. An yi kira ga gwamnati, da ta dauki matakai kan lamarin dan tsafta kafafen...
Bidiyo: Ni ba ‘yar Iska bace: Mansurah Isah ta bayyana hali na gari da yasa Sani Danja ya aureta

Bidiyo: Ni ba ‘yar Iska bace: Mansurah Isah ta bayyana hali na gari da yasa Sani Danja ya aureta

Duk Labarai
Tsohuwar tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah ta bayyana dalilin da yasa Tsohon Mijinta, Sani Danja ya aureta. Mansurah ta bayyana hakanne a wata hira da BBChausa ta yi da ita inda take cewa ita ba 'yar Iska bace. Tace da ita 'yar iska ce da Sani Danja bai Aureta ba. Kalli Bidiyon hirar: https://www.tiktok.com/@musaddeeqq_haysam/video/7508388274101046534?_t=ZM-8wfWYscDyDt&_r=1 Mansurah dai ta tabbatar da cewa Aurenta na biyu ya mutu ne a hirar da BBC inda tace mijin nata yaudararta yayi.
Fada Saboda Budurwa yasa an yi asarar rai a Kano

Fada Saboda Budurwa yasa an yi asarar rai a Kano

Duk Labarai
Rahotanni daga Kano sun ce fada da ya barke tsakanin matasan kauyukan Faruruwa dana Tarandai dake karamar hukumar Takai ta jihar yasa an yi asarar rai. Lamarin ya farune a kasuwar garin Faruruwa ranar 23 ga watan Mayu da misalin karfe 7:45 p.m. An yi fadanne ranar Kasuwar garin inda aka kona runfunan Kasuwa da dama. Rahoton yace wani me suna Sani Yunusa, 28 daga kauyen Toho Diribo dake karamar hukumar Takai ya je wajan budurwarsa dake kauyen Tarandai. Saidai matasa sun afka masa da duka da itace. Tuni aka aika da jami'an tsaro yankin dan su kwantar da tarzomar. Rahoton yace ana kokarin kama wadanda suka fara tada tarzomar dan yi musu hukunci.
Bidiyon matar aure tana lalata da wani ya bayyana inda mata suka fito zanga-zanga

Bidiyon matar aure tana lalata da wani ya bayyana inda mata suka fito zanga-zanga

Duk Labarai
Bidiyon matar aure ya bayyana a kafafen safa zumunta inda aka ganta tana lalata da wani mutum. Matar dai ta fito ne daga jihar Anambra. Lamarin yasa matan yankin da take suka fito zanga-zanga inda suke cewa tana kokarin kwace musu maza. Matar dai da aka yi hira da ita tace taĺauci ne yasa ta ta aikata hakan. Tace kuma cin zarafin da mijinta yake mata ya taimaka sosai wajan halin data samu kanta.
Matashiyar ƴar gwaggwarmaya Hamdiyya Shareef ta koma gidansu bayan zargin sace a Sakkwato

Matashiyar ƴar gwaggwarmaya Hamdiyya Shareef ta koma gidansu bayan zargin sace a Sakkwato

Duk Labarai
Rundunar ƴansandan Najeriya ta samu nasarar hada matashiyar ƴar gwagwarmayan nan, Hamdiyya Shareef da mahaifan ta a Sakkwato bayan batan da ta yi a ranar Laraba. Hamdiyya, wadda ta shahara wajen fafutukar ilimin ‘yan mata da kare hakkin matasa, ta bace a wani hali da ba a san ainihin dalilinsa ba, lamarin da ya tayar da hankulan mahaifan ta da dangin ta da masu goyon bayanta. A cewar Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Sokoto, hadin gwiwa da hanzarin tattara bayanan sirri ne suka taimaka wajen gano inda take cikin koshin lafiya. Kakakin rundunar ya yaba wa ‘yan kasa bisa hadin kan da suka bayar tare da jaddada kudirin rundunar na kare duk wani dan Najeriya, musamman matasa masu rauni. ‘Yan uwanta, cike da hawaye da farin ciki, sun bayyana godiya ga ‘yan sanda da duk wanda ya tsaya musu a ...
Ku Daina Wahalar da kanku an rubuta sakamakon zaben shekarar 2027>>Sowore ya gayawa ‘yan Najeriya

Ku Daina Wahalar da kanku an rubuta sakamakon zaben shekarar 2027>>Sowore ya gayawa ‘yan Najeriya

Duk Labarai
Mawallafin jaridar Sahara reporters, Omoyele Sowore kuma dan siyasa ya bayyana cewa an riga an rubuta sakamakon zaben shekarar 2027. Ya bayyana hakane a wata hira da kafar Vanguard ta yi dashi. Inda yace abu daya kawai da 'yan Najeriya zasu yi shine su yi zanga-zanga dan samun zabe me kyau amma tsarin zaben da ake dashi bai da kyau Kuma ya bayyana cewa, ba zai hada kai da Peter Obi ba a zaben shekarar 2027 ba.
Wasu Daga Cikin Falalar Goman Farko Na Watan Zulhijja

Wasu Daga Cikin Falalar Goman Farko Na Watan Zulhijja

Duk Labarai
Wasu Daga Cikin Falalar Goman Farko Na Watan Zulhijja. …jama'a mu yada (sharing) wannan sako domin amfanar sauran jama'a 1) Allah Ya yi rantsuwa da su a cikin alQurani. Qur'an 89:2. 2) Sune Ayyamun Ma'alumat da Allah ya umurci ayi ambaton sa a ciki a suratul Hajj Qur'an 22: 28. 3) Aiki a cikin su yafi falala da lada da soyuwa ga Allah akan duk sauran kwanakin shekara. Bukhari no.926. 4) Ana so a yawaita Subhanallah, Walhamdulilllah, wallahu Akbar wa Lailaha illallah da karatun al-Qurani. Bukhari ya ruwaito. 5) Ana so a bayyana ambaton Allah a ciki domin a tunawa wanda yamanta. Abdullahi Ibn Umar da Abu-Hurairah sun kasance suna shiga kasuwa suna kabbara jamaa na kabbara da kabbarar su. Bukhari ya ruwaito . 6) Aikin Hajji yana cikin Ayukka mafi falala a cikin wadann...
DA ƊUMI-ƊUMI: Atiku, Peter Obi, Amaechi, Kashim Ibrahim-Imam da sauran manyan shugabanni sun fara wani babban taron haɗaka yanzu haka a Abuja, domin tsara yadda za su kayar da Tinubu a zaɓen 2027

DA ƊUMI-ƊUMI: Atiku, Peter Obi, Amaechi, Kashim Ibrahim-Imam da sauran manyan shugabanni sun fara wani babban taron haɗaka yanzu haka a Abuja, domin tsara yadda za su kayar da Tinubu a zaɓen 2027

Duk Labarai
Ana Gudanar Da Taron Haɗaka Tsakanin Manya 'Yan Siyasar Jam'iyyun Hamayya A Nijeriya. A wajen taron an hango Tsohon Mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa Peter Obi, shugaban BOT na PDP, Adolphus Wabara, da sauran manyan 'yan siyasa da masu ruwa da tsaki. An yiwa taron laƙabi da (National Political Consultative Group (North) . Ana sa ran tattaunawa kan makomar siyasar Arewa da haɗa ƙarfi don fuskantar manyan zaɓuka masu zuwa a 2027. Me zaku ce?