Tuesday, March 31
Shadow
Inna lillahi wa inna ilaihi Raji’un: Jirgin saman Sojojin Najeriya ya kara yin kuskure akan farar Hula

Inna lillahi wa inna ilaihi Raji’un: Jirgin saman Sojojin Najeriya ya kara yin kuskure akan farar Hula

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Naija na cewa, jirgin sojin saman sojojin Najeriya ya sake kuskurewa akan farar hula a jihar Naija. Lamarin ya farune a Kurgi dake karamar hukumar Kuriga. Lamarin ya farune ranar 25 ga watan Janairu wanda ya yi sanadiyyar jikkatar mutane da dama. An jima dai ana samun irin wannan kuskuren akan farar Hula a Najeriya.
Kalli Bidiyon matakin da ‘yan Kasuwar Onitsha suka dauka bayan da Gwamnan jihar ya kulle kasuwar saboda suna kin fitowa kasuwa ranar Litinin

Kalli Bidiyon matakin da ‘yan Kasuwar Onitsha suka dauka bayan da Gwamnan jihar ya kulle kasuwar saboda suna kin fitowa kasuwa ranar Litinin

Duk Labarai
A jiyane da muka kawo muku Rahoton cewa, Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo ya kulle kasuwar Onitsha na tsawon sati daya. Dalili shine 'yan kasuwar na biyewa tshageran dake hanasu bude shaguna ranar Litinin. A martanin 'yan kasuwar, sun je gadar Onitsha inda suka ajiye motocinsu suka hana shiga da fita garin dan nuna fushinsu da matakin da gwamnan ya dauka. https://twitter.com/i/status/2016412406876897514
Kalli Bidiyon: Na shiga Musulunci amma abin mamaki Musulmai sai Izgili suke min suna cewa Musuluncin karya nake, da gayamin Munanan Kalamai>>Inji Maryam Zool

Kalli Bidiyon: Na shiga Musulunci amma abin mamaki Musulmai sai Izgili suke min suna cewa Musuluncin karya nake, da gayamin Munanan Kalamai>>Inji Maryam Zool

Duk Labarai
Tauraruwar Tiktok, Maryam Zool wadda tace ta shiga Musulunci ta bayyana cewa ta hadu da abinda bata yi tsammani ba. tace tasha Kiristoci ne zasu rika mata Izgili amma sai gashi Musulmai ne suka rika zaginta da gaya mata Arniya da cewa wai Musuluncin qarya take. Tace dan haka yanzu ta koma Kirista. https://www.tiktok.com/@fcbaby246/video/7599853844775898386?_r=1&_t=ZS-93Rrsm6AzWz
Kalli Bidiyon: Dalilin da Abba ya bayar na komawarsa APC ya sa mutane rike baki

Kalli Bidiyon: Dalilin da Abba ya bayar na komawarsa APC ya sa mutane rike baki

Duk Labarai
An wani Bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta, anga Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf na bayyana cewa ba'a ja da Gwamnatin tarayya. Ya bayyana cewa, kudaden shiga da suke samu daga gwamnatin tarayya ne suke amfani dasu wajan yiwa al'umma aiki. https://twitter.com/i/status/2016272428893151566 Wasu sun fassara wannan kalami nasa da cewa, ashe kudi ne suka sanya ya koma jam'iyyar APC din.
Kalli Bidiyon abin Kunyar da ya faru da gwamnan jihar Adamawa, wanda har sai da jami’in tsaronsa ya fashe da dariya

Kalli Bidiyon abin Kunyar da ya faru da gwamnan jihar Adamawa, wanda har sai da jami’in tsaronsa ya fashe da dariya

Duk Labarai
Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri ya je garin Ganye mahaifar Atiku Abubakar inda yake tallar jam'iyyar PDP. Saidai a wajan yana jawabi ana masa ehon bamayi. Daga baya abin ya bashi haushi ya mayar da martani me zafi. A karshe dai da ya ga jawabin nasa ba zai yiyu ba, sai yace DJ ya saka mai kida, inda ya dan taka rawa, ya kama gabansa, ya fice daga wajan taron. https://twitter.com/i/status/2016237773657649323
Kalli Bidiyon da Duminsa: Shugaban kasa, ji abinda ya faru da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bayan da yayi Tuntube ya fadi a kasar Turkiyya

Kalli Bidiyon da Duminsa: Shugaban kasa, ji abinda ya faru da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bayan da yayi Tuntube ya fadi a kasar Turkiyya

Duk Labarai
Biyo bayan Tuntuben da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi ya fadi a kasar Turkiyya, yayin da yake tafiya shi da shugaban kasar Turkiyyan Recep Erdogan. Fadar shugaban kasa ta fitar da sanarwar cewa, shugaba Tinubu yana cikin koshin Lafiya. Sanarwar wadda ta fito daga bakin me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya bayyana cewa, yanayin yanda aka shimfida kafet din da shugaba Tinubu ke tafiya akai ne bai shimfidu da kyau ba shiyasa yayi Tuntuben. Sanarwar tace shugaba Tinubu bai ji ciwo a faduwar da yayi ba, kuma yanzu haka ya ci gaba da ziyarar aikin da yake a kasar ta Turkiyya. https://twitter.com/i/status/2016166532305273212