Saturday, December 6
Shadow
Na bar Gidanmu ina da kananan Shekaru sosai kuma banda Ko Sisi amma yanzu Allah ya min daukaka da Arziki>>Inji Rahama Sadau

Na bar Gidanmu ina da kananan Shekaru sosai kuma banda Ko Sisi amma yanzu Allah ya min daukaka da Arziki>>Inji Rahama Sadau

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Rahama Sadau ta bayyana cewa tana da kananan shekaru sosai ta bar gidansu ta shiga harkar film a lokacin bata da ko sisi. Tace Amma cikin Ikon Allah sai gata ta samu Daukaka da Arziki har ta dauki wasu aiki. Ta bayyana hakane a wani Bidiyo inda take karfafa 'ya'ya mata su bi burin zuciyarsu sannan su nuna jajircewa. https://www.tiktok.com/@rahamasadaufanspage0/video/7570452687980907794?_t=ZS-91HlFZW2Ajp&_r=1
Wallahil Azim Buhari ya zo min a mafarki, da fararen kaya da Dogon gashi, Fuskarsa cike da annuri yace min ya gode da addu’o’in da nake masa>>Inji tsohuwar Hadimar Buhari, watau Baby Buhari

Wallahil Azim Buhari ya zo min a mafarki, da fararen kaya da Dogon gashi, Fuskarsa cike da annuri yace min ya gode da addu’o’in da nake masa>>Inji tsohuwar Hadimar Buhari, watau Baby Buhari

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wata tsohuwar hadimar tsohon shugaban kasa da ake kira da Beby Buhari ta yi ikirarin cewa, Marigayi tsohon shugaban kasar ya bayyana gareta a mafarki. Ta wallafa a shafinta na X cewa, ta ga Buhari a mafarki da fararen kaya da Dogon gashi fuskarsa cike da annuri yace mata ya gode da addu'o'in da take masa. Tace lamarin ya bata mamaki matuka. https://twitter.com/baby_done1/status/1987806516519309398?t=wN6Xt6jDkyTdHmi-dqnabw&s=19
Bharazanar Trump tasa mun gane wadanda basa kishin kasa da Munafukan cikinmu>>Inji Sheikh Gumi

Bharazanar Trump tasa mun gane wadanda basa kishin kasa da Munafukan cikinmu>>Inji Sheikh Gumi

Duk Labarai
Malamin addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya bayyana cewa, Barazanar da shugaban kasar Amurka, Donald Trump yawa Najeriya tasa an gano marasa kishin kasa da Makiya. Ya bayyana hakane a shafinsa na Facebook. A baya dai malam yayi kira ga Shugaba Trump da ya janye kalamansa akan Najeriya sannan kuma ya bayar da hakuri inda yace Shugaba Tinubu ya yanke hulda da Amirka idan Trump din yaki yin hakan.
Na yi mafarkin an sake yin Muslim Muslim a Najeriya, El-Rufai ya zama shugaban kasa, Rauf Aregbesola ya zama mataimakinsa>>Inji Dan majalisa, Nuhu Sada

Na yi mafarkin an sake yin Muslim Muslim a Najeriya, El-Rufai ya zama shugaban kasa, Rauf Aregbesola ya zama mataimakinsa>>Inji Dan majalisa, Nuhu Sada

Duk Labarai
Tsohon Dan majalisa na majalisar jihar Kaduna daya wakilci Zaria, Hon. Nuhu Sada ya bayyana cewa, idan yayi mafarki, mafarkin yakan zama gaskiya. Yace kuma yayi mafarkin tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya zama shugaban Najeriya kuma Rauf Aregbesola ya zama mataimakinsa.
Shugaban Amurka Trump yace zai yi Amfani da kudaden Harajin da ya samu daga kasashen Duniya wajan rabawa ‘yan kasar Dala $2000 kowannensu

Shugaban Amurka Trump yace zai yi Amfani da kudaden Harajin da ya samu daga kasashen Duniya wajan rabawa ‘yan kasar Dala $2000 kowannensu

Duk Labarai
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, zai Rabawa mutanen kasarsa dala $2000 kowanne daga kudin Harajin da ya tara daga hannun kasashen Duniya. Ya bayyana hakane a shafinsa na Truth social inda yace kasarsa ce kasa da aka fi girmamawa a tsakanin kasashen Duniya Sannan ya yi alkawarin yin amfani da kudin Harajin wajan biyan bashin da ake bin kasar Amurka. Saidai da yawa 'yan kasar ta Amurka na shakka akan wannan ikirari nasa.
Allah ya riga ya kaddarowa Atiku ba zai zama Shugaban Najeriya ba dan haka ya hakura kawai>>Inji Sarkin Legas, Oba Rilwan Akiolu

Allah ya riga ya kaddarowa Atiku ba zai zama Shugaban Najeriya ba dan haka ya hakura kawai>>Inji Sarkin Legas, Oba Rilwan Akiolu

Duk Labarai
Sarkin Legas, Oba Rilwan Akiolu ya bayyana cewa Allah ya riga ya kaddarowa Atiku Abubakar cewa ba zai zama shugaban kasar Najeriya ba. Yayi kira ga Atiku da ya hakura da kaddarar da Allah ya doro masa cewa ba zai zama shugaban Najeriya. Atiku dai tin a shekarar 1992 yake neman takarar shugabancin Najeriya amma bai samu ba. Ya bayyana hakane ga manema labarai a fadarsa yayin da yake bikin cika shekaru 22 da hawa karagar sarautar Birnin na Legas. Yace shi kuma Tinubu zabin Allah ne dan haka yana kira ga 'yan Najeriya da su goya masa baya.
Gwamnatin Tarayya ta ciwo bashi fiye da yanda ta yi niyyar Ciyowa

Gwamnatin Tarayya ta ciwo bashi fiye da yanda ta yi niyyar Ciyowa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin Tarayya ta ciwo bashi fiye da yanda ta yi niyyar ciyowa a shekarar 2025. A kasafin kudin shekarar 2025, Gwamnati ta yi niyyar ciwo bashin Naira Tiriliyan 13.08 saidai zuwa yanzu har ta ciwo bashin Naira Tiriliyan 17.36. Hakan na nufin Gwamnatin ta ciwo bashin Naira Tiriliyan N6.06 sama da abinda ta yi niyyar ciyowa a wannan shekarar tun ma shekarar bata kare ba. Gwamnatin taci bashin naira Tiriliyan N15.8 daga cikin gida Najeriya sai kuma bashin Naira Tiriliyan 1.56 daga kasashen waje. A satin daya gabata ne dai Gwamnatin ta bayyana aniyar son ciwo bashin Naira Tiriliyan N3.384 daga kasashen Turai.
Dan majalisar Tarayya daga jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa ya jefar da Jar Hula NNPP ya koma jam’iyyar APC

Dan majalisar Tarayya daga jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa ya jefar da Jar Hula NNPP ya koma jam’iyyar APC

Duk Labarai
Dan majalisar wakilai ta tarayya, Abdulmumin Jibrin Kofa dake wakiltar mazabun Kiru/Bebeji ya bar jam'iyyar NNPP ya kpma jam'iyyar APC. Ya bayyana hakan ne ranar Litinin a sakon da ya fitar a shafinsa na sada zumunta. Hakan na zuwane watanni 2 bayan da jam'iyyar NNPP ta koreshi bisa zargin yana mata zagon kasa da kuma kin biyan kudaden harajin jam'iyyar. Komawarsa APC bata zowa mutane da bazata ba musamman lura da yanda yake da alaka me kyau da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Ya bayyana cewa yana goyon bayan Tinubu ya zarce a 2027 sannan kuma yace malamai 2000 ne sukawa shugaba Tinubu da Najeriya addu'a a mazabarsa.