Sunday, February 15
Shadow
Wata Sabuwa: Ana rade-radin akwai yiyuwar tsohon Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar zai koma jam’iyyar ADC

Wata Sabuwa: Ana rade-radin akwai yiyuwar tsohon Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar zai koma jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Jigawa na cewa, akwai yiyuwar Tsohon gwamnan jihar kuma tsohon Ministan tsaro, Abubakar Badaru ,ai bar jam'iyyar APC zuwa ADC. Rahoton yace hakan na zuwane yayin da baraka ke ci gaba da bayyana a tsakanin tsohon Ministan da magajinsa gwamna me ci na yanzu, watau Namadi. https://twitter.com/i/status/2008108500493197502
Da Duminsa: An samu Baraka a jam’iyyar APC, ji maganganu marasa dadi da Wike yake gayawa shugaban kasa

Da Duminsa: An samu Baraka a jam’iyyar APC, ji maganganu marasa dadi da Wike yake gayawa shugaban kasa

Duk Labarai
Wani Bidiyon Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya bayyana inda aka jishi yana wata barazana. An ji Wike na barazanar ne a wajan wani taron siyasa a jiharsa. Ya bayyana cewa mutum kada ya zo ya kawo musu abinda ba shi kenan ba a jihar Rivers. Wike bai fadi da wanda yake ba inda yace mutum ya tambayi abinda ya faru da wadanda suka yi yunkurin yiwa jihar Rivers kutse a baya. saidai wasu sun ce da sakataren Jam'iyyar APC yake inda wasu kuma ke cewa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yake. https://twitter.com/i/status/2008170575286419869
Da Duminsa: Manchester United ta kori Ruben Amorim a matsayin kocinta

Da Duminsa: Manchester United ta kori Ruben Amorim a matsayin kocinta

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kungiyar Manchester United ta kori Ruben Amorim a matsayin kocinta. Hakan na zuwane bayan da ya kwashe watanni 14 yana matsayin kocin Kungiyar. Dangantaka ta yi tsami tsakanin dan kasar Portugal din me shekaru 40 da kungiyar a 'yan kwanakinnan. Manchester United dai a yanzu tana matsayi na 6 akan teburin Premier league. Manchester United ta sanar da Darren Fletcher a matsayin kocin wucin gadi.
Kudaden Bashin da Shugaba Tinubu ke karbowa da ‘yan Najeriya yake baiwa su yi Jari da an samu saukin Rayuwa>>Inji Peter Obi

Kudaden Bashin da Shugaba Tinubu ke karbowa da ‘yan Najeriya yake baiwa su yi Jari da an samu saukin Rayuwa>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party a zaben shekarar 2023 data gabata, Peter Obi ya bayyana cewa, kudaden da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ke karbowa Bashi, da Tallafawa 'yan Najeriya yake yi da jari da ba haka ba. Yace ana ta cewa babu kudi amma kuma gwamnati na ta kara ciwo bashi. Ya ce wadanda aka baiwa su yi jari zasu samarwa wasu aikin yi ta hakane za'a samu saukin talaucin da ake fama dashi a kasarnan. https://twitter.com/i/status/2007903277632069826
Da Duminsa: Fadar Shugaban kasa ta yi magana kan abin kunyar da ake zargin shugaba Tinubu da yi

Da Duminsa: Fadar Shugaban kasa ta yi magana kan abin kunyar da ake zargin shugaba Tinubu da yi

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta yi martani kan abin kinyar da ake zargin shugaban da yi ta hanyar wallafa Hoton AI a shafinsa na X. Me magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya bayyana cewa, Hoton bana AI bane. Yace da gaske shugaba Tinubu da Takwaransa, Paul Kagame suna kasar Faransa kuma sun gana. Yace wanda ya daukesu hotonne wayarsa bata daukar hoto me kyau shine yayi Amfani da AI ya gyara hoton. Lamarin hoton dai ya jawo cece-kuce sosai a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/i/status/2008092644266656148