Sojoji Sun Ķàma Wañi Dan Shekàŕu 55 Mai Gaŕkuwa Da Mutane A Ķano
An kama shine a kauyen Sumana dake karamar hukumar Tudun Wada a Kano, inda aka gano makàmai a wuŕinsà.
Bidiyon tsohon gwamnan jihar Kaduna, ya yin da yake jiran jirgi a Filin jirgin sama na Cairo kasar Egypt, domin shillawa Abuja.
Kalli Bidiyon a kasa:
https://www.tiktok.com/@n.elrufai/video/7496050348981898502?_t=ZM-8vkQHC3WDG1&_r=1
Da yawa sun yi masa fatan Alheri.
Daruruwan magoya bayan dakatatcen gwamnan jihar River Siminalayi Fubara ne suka fito zanga-zanga a yau Talata, su na masu kira da a mayar da shi kan kujerar sa ta gwamna.
RFI ta rawaito cewa sun dai faro tattakin ne daga kan hanyar Aggrey, inda suke rike da alluna masu ɗauke da rubuce-rubucen cewa "muna tare da gwamna Sim Fubara", "muna buƙatar a maido mana da gwamnanmu da muka zaɓa", da dai sauransu.
Wannan ce dai gangami na baya-bayan nan da magoya bayan gwamnan suka gudanar, tun bayan dakatar da shi da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya yi a ranar 18 ga watan daya gaba.
A tattakin da su ke yi, sun riƙa rera wakoki da kade-kade da raye-raye tare da rera addu'o'in fatan a dawo da Fubara kan karagar sa ta mulkin jihar Rivers.
Dakatarwar dai ta shafi mataimakiyarsa Ngozi Odu da...
An sanar da ranar da za a binne Fafaroma.
Fadar Vatican ta tabbatar da cewa za a yi jana'izar marigayi, Fafaroma Francis da ƙarfe 8 na safe agogon GMT, a ranar Asabar mai zuwa.
Hakan na zuwa ne yayin da fadar ta fitar da bidiyon da ke nuna mamacin kwance a cikin akwatin gawa, a cocin Casa Santa Marta da ke gidansa.
Bidiyon ya nuna gawar Fafaroma sanye da jar doguwar riga da hularsa ta fafaroma da kuma carbi a hannunsa.
A ranar Laraba ne za a mayar da gawar St Peter's Basilica, inda za a ajiye shi domin mutane su yi masa bankwana har zuwa ranar Asabar da za a binne shi.
Fafaroma Francis ya mutu ne a ranar Litinin yana da shekaru 88 a duniya, sakamakon bugun zuciya.
Rahotanni Sun tabbatar da cewa Ganduje ya shiga ɗimuwa yakasa zaune yakasa tsaye Bisa jin cewar Kwankwaso Zai shiga cikin jam'iyyar Apc, An shiga fargaba a APC kan batun dawowar Kwankwaso jam'iyyar
A yayin da a ke ci gaba da rade-radin yiwuwar sauya shekar tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso zuwa jam’iyyar mai mulki ta APC, wasu majiyoyi daga cikin jam’iyyar sun bayyana cewa wannan yunkuri na tsohon gwamnan jihar Kano ya haifar da fargaba a cikin jam’iyyar.
Majiyoyin jam’iyyar sun bayyana wa jaridar TRIBUNE cewa wannan yunkuri da ake cewa ya samo asali ne daga yarjejeniya tsakanin shugaban kasa Bola Tinubu da jagoran na NNPP, na janyo rashin jin dadi a bangaren shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, da kuma Sanata Barau Jibrin, ...
Tarihin Yunkurin Juyin Mulkin Ďa Janar Babangida Ya Tsàĺĺakè Rijiya Da Baya A Shekarar 1990,
..da kuma wasu jihohin Aŕewa guda biýar da aka sanar da ķorar su daga Nijeriya a lokacin juyin mulkin
Daga Muhammad Cisse
A rana mai kamar ta yau ne 22 ga watan Afrilu 1990. An yi yunkurin juyin mulkin a Nijeriya, wani yunkuri ne na juyin mulkin da sojoji suka yi a Nijeriya a ranar 22 ga Afrilun 1990, a lokacin da wani bangare na hafsoshin Sojin kasar, karkashin jagorancin Manjo Gideon Orkar, suka yi yunkurin hambarar da gwamnatin Janar Ibrahim Babangida.
Dakarun Sojoji masu yunkurin juyin mulkin sun kwace gidan rediyon FRCN da ofisoshin sojoji daban-daban a kewayen Legas, ciki har da hedkwatar sojoji da gidan shugaban kasa a Barrack Dodan. Babangida yana wurin lokacin da aka kai hari a...
Sheik Farfesa Isa Pantami Ya Kaiwa Sheik Sani Yahaya Jingir Ziyarar Ta'aziyar Rasuwar Shaykh Saidu Hassan Jingir A Jos
Sheik Pantami ya yi fatan Allah Ya yi rahama ga Malam, tare da sauran iyayenmu da malamanmu, da zurriyyarmu.
Aishat Aliyu Mamancy Ta Bar Wasiyya Cewa "Ina Roko Duk Ranar Da Labarin Mutuwata Ya Riske Ku, Don Allah Ku Roka Min Rahamar Ubangiji"
Yau gashi an wayi gari ta rasu, inda aka yi jana'izarta a yau Talata a Kano, kamar yadda Rariya ta samu labari.
Allah Ya gafarta mata.
Hukumar Hisbah a Kano ta lalata wajan da aka rika yada rade-radin cewa wai an ga sahun Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) a Kano.
Wajan dai yana Dakata ne inda aka ga bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sadarwa mutane suna rububin sha da wanka da ruwan wajan.
Mataimakin kwamandan Hisbah na jihar Kano, Muhahideen Aminudeen ya bayyana cewa ko da suka ji labari, sun je wajan inda suka ilimantar da mutanen wajen cewa wannan ikirari karyane.
https://twitter.com/bapphah/status/1914187045083247072?t=sxDEREGOf_DmRbxUOoqQFA&s=19
Sun gayawa mutanen cewa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) bai taba zuwa Afrika ba.
Ya jawo hankalin iyaye da su rika baiwa 'ya'yansu ilimi na Addini dan su rika banbance gaskiya da karya.
Ya kuma bayyana cewa shan irin wannan ruwa ma na da hadari ga ...
Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya bayyana cewa duk wani dan siyasar Arewa da ya taba rike mukami a cikin shekaru 20 da suka gabata, yana da hannu wajan lalacewar yankin.
Yace matsalar Arewa ba a cikin shekaru 2 da suka gabata ta fara ba, ta dade ana fama da ita.
Ya kara da cewa, kuma duk wani dan siyasa da ya taba rike mukami a yankin ya kamata ya fito ya baiwa mutane hakuri saboda sun gaza.
Yace a lokacin Mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya saki kudi sosai na tallafi yace amma da yake in dambu yayi yawa baya jin mai, hakan bai kawo karshen matsalar ba.
Uba Sani yace mutane su yi hankali da 'yan siyasar da ana tare dasu a baya amma su rika warewa suna cewa wai su sun tuba.
Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a Trust TV.